< 2 Chronicles 15 >

1 The Spirit of God came on Azariah the son of Oded.
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Azariya ɗan Oded.
2 He went out to meet Asa, and said to him, “Hear me, Asa, and all Judah and Benjamin! Yahweh is with you while you are with him; and if you seek him, he will be found by you; but if you forsake him, he will forsake you.
Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.
3 Now for a long time Israel was without the true God, without a teaching priest, and without law.
Tun da daɗewa Isra’ila ba su da Allah na gaskiya, babu firist da zai koyar, kuma babu doka.
4 But when in their distress they turned to Yahweh, the God of Israel, and sought him, he was found by them.
Amma cikin wahalarsu suka juya ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka kuma neme shi, suka kuwa same shi.
5 In those times there was no peace to him who went out, nor to him who came in; but great troubles were on all the inhabitants of the lands.
A waɗancan kwanaki akwai hatsari a yin tafiye-tafiye, gama dukan mazaunan ƙasashe suna cikin babbar damuwa.
6 They were broken in pieces, nation against nation, and city against city; for God troubled them with all adversity.
Wata ƙasa takan murƙushe wata, wani birni kuma yakan murƙushe wani, domin Allah ya wahalshe su da kowace irin damuwa.
7 But you be strong! Don’t let your hands be slack, for your work will be rewarded.”
Amma game da ku, ku ƙarfafa kada ku fid da zuciya, gama za a ba ku ladan aikinku.”
8 When Asa heard these words and the prophecy of Oded the prophet, he took courage, and put away the abominations out of all the land of Judah and Benjamin, and out of the cities which he had taken from the hill country of Ephraim; and he renewed Yahweh’s altar that was before Yahweh’s porch.
Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
9 He gathered all Judah and Benjamin, and those who lived with them out of Ephraim, Manasseh, and Simeon; for they came to him out of Israel in abundance when they saw that Yahweh his God was with him.
Sa’an nan ya tattara dukan Yahuda da Benyamin da kuma mutane daga Efraim, Manasse da Simeyon waɗanda suke zaune a cikinsu, gama jama’a mai girma ta zo wurinsa daga Isra’ila sa’ad da suka ga cewa Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
10 So they gathered themselves together at Jerusalem in the third month, in the fifteenth year of Asa’s reign.
Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta mulkin Asa.
11 They sacrificed to Yahweh in that day, of the plunder which they had brought, seven hundred head of cattle and seven thousand sheep.
A lokacin suka miƙa hadaya bijimai ɗari bakwai da tumaki da kuma awaki dubu bakwai ga Ubangiji daga ganimar da suka dawo da ita.
12 They entered into the covenant to seek Yahweh, the God of their fathers, with all their heart and with all their soul;
Suka yi alkawari don su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, da dukan zuciyarsu da kuma dukan ransu.
13 and that whoever would not seek Yahweh, the God of Israel, should be put to death, whether small or great, whether man or woman.
Aka kashe dukan waɗanda ba su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila ba, ko ƙarami ko babba, namiji ko ta mace.
14 They swore to Yahweh with a loud voice, with shouting, with trumpets, and with cornets.
Suka yi rantsuwa ga Ubangiji da babbar murya, da ihu da garayu da ƙahoni.
15 All Judah rejoiced at the oath, for they had sworn with all their heart and sought him with their whole desire; and he was found by them. Then Yahweh gave them rest all around.
Dukan Yahuda suka yi farin ciki game da rantsuwar domin sun yi rantsuwar gabagadi. Suka nemi Allah da gaske, suka kuma same shi. Saboda haka Ubangiji ya ba su hutu a kowane gefe.
16 Also Maacah, the mother of Asa the king, he removed from being queen mother, because she had made an abominable image for an Asherah; so Asa cut down her image, ground it into dust, and burned it at the brook Kidron.
Sarki Asa ya tuɓe mahaifiyar mahaifiyarsa daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, domin ta gina ginshiƙin banƙyama na Ashera. Asa ya rurrushe shi, ya farfasa shi ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
17 But the high places were not taken away out of Israel; nevertheless the heart of Asa was perfect all his days.
Ko da yake bai kawar da masujadan kan tudu daga Isra’ila ba, zuciyar Asa ta cika da bin Ubangiji dukan kwanakinsa.
18 He brought the things that his father had dedicated and that he himself had dedicated, silver, gold, and vessels into God’s house.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyaki a haikalin Allah waɗanda shi da mahaifinsa suka keɓe.
19 There was no more war to the thirty-fifth year of Asa’s reign.
Ba a ƙara yin yaƙi ba sai a shekara ta talatin da biyar ta mulkin Asa.

< 2 Chronicles 15 >