< 1 Thessalonians 5 >

1 But concerning the times and the seasons, brothers, you have no need that anything be written to you.
To,’yan’uwa, game da lokuta da ranaku, ba ma bukata mu rubuta muku,
2 For you yourselves know well that the day of the Lord comes like a thief in the night.
gama kun sani sarai cewa ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo da dare.
3 For when they are saying, “Peace and safety,” then sudden destruction will come on them, like birth pains on a pregnant woman. Then they will in no way escape.
Yayinda mutane suke cewa, “Akwai salama da zaman lafiya,” hallaka za tă auko musu farat ɗaya, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba za su kuwa tsira ba.
4 But you, brothers, aren’t in darkness, that the day should overtake you like a thief.
Amma ku,’yan’uwa, ba kwa cikin duhu da wannan rana za tă zo muku ba zato kamar ɓarawo.
5 You are all children of light and children of the day. We don’t belong to the night, nor to darkness,
Dukanku’ya’yan haske ne da kuma’ya’yan rana. Mu ba mutanen dare ko na duhu ba ne.
6 so then let’s not sleep, as the rest do, but let’s watch and be sober.
Saboda haka fa, kada mu zama kamar saura, waɗanda suke barci, sai dai mu zama masu tsaro da masu kamunkai.
7 For those who sleep, sleep in the night; and those who are drunk are drunk in the night.
Gama masu barci, da dad dare suke barci, masu sha su bugu kuwa, da dad dare suke buguwa.
8 But since we belong to the day, let’s be sober, putting on the breastplate of faith and love, and for a helmet, the hope of salvation.
Amma da yake mu na rana ne, bari mu zama masu kamunkai, sanye da bangaskiya da ƙauna kamar sulke, begen cetonmu kuma kamar hular kwano.
9 For God didn’t appoint us to wrath, but to the obtaining of salvation through our Lord Jesus Christ,
Gama Allah bai naɗa mu don mu sha fushi ba, sai dai mu sami ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
10 who died for us, that, whether we wake or sleep, we should live together with him.
Ya mutu saboda mu domin, ko muna a faɗake ko muna barci, mu kasance tare da shi.
11 Therefore exhort one another, and build each other up, even as you also do.
Saboda haka ku ƙarfafa juna ku kuma gina juna, kamar dai yadda kuke yi.
12 But we beg you, brothers, to know those who labor among you, and are over you in the Lord and admonish you,
To, muna roƙonku,’yan’uwa, ku girmama waɗanda suke aiki sosai a cikinku, waɗanda suke bisanku cikin Ubangiji da kuma waɗanda suke yin muku gargaɗi.
13 and to respect and honor them in love for their work’s sake. Be at peace among yourselves.
Ku riƙe su da mutunci sosai cikin ƙauna saboda aikinsu. Ku yi zaman lafiya da juna.
14 We exhort you, brothers: Admonish the disorderly; encourage the faint-hearted; support the weak; be patient toward all.
Muna kuma gargaɗe ku,’yan’uwa, ku gargaɗe waɗanda suke zaman banza, ku ƙarfafa masu raunanar zuciya, ku taimaki marasa ƙarfi, ku yi haƙuri da kowa.
15 See that no one returns evil for evil to anyone, but always follow after that which is good for one another and for all.
Ku tabbata cewa kada kowa yă rama mugunta da mugunta, sai dai kullum ku yi ƙoƙarin yin wa juna alheri da kuma dukan mutane.
16 Always rejoice.
Ku riƙa farin ciki kullum;
17 Pray without ceasing.
ku ci gaba da yin addu’a;
18 In everything give thanks, for this is the will of God in Christ Jesus toward you.
ku yi godiya cikin kowane hali, gama wannan shi ne nufin Allah dominku cikin Kiristi Yesu.
19 Don’t quench the Spirit.
Kada ku danne aikin Ruhu.
20 Don’t despise prophecies.
Kada ku rena annabci,
21 Test all things, and hold firmly that which is good.
amma ku gwada kome, ku riƙe abin da yake mai kyau,
22 Abstain from every form of evil.
ku ƙi kowace mugunta.
23 May the God of peace himself sanctify you completely. May your whole spirit, soul, and body be preserved blameless at the coming of our Lord Jesus Christ.
Bari Allah da kansa, Allah na salama, yă tsarkake ku sarai. Bari dukan ruhunku, ranku, da kuma jikinku su zama marar aibi a dawowar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
24 He who calls you is faithful, who will also do it.
Wannan wanda ya kira ku mai aminci ne zai kuwa aikata.
25 Brothers, pray for us.
’Yan’uwa, ku yi mana addu’a.
26 Greet all the brothers with a holy kiss.
Ku gaggai da dukan’yan’uwa da sumba mai tsarki.
27 I solemnly command you by the Lord that this letter be read to all the holy brothers.
Na gama ku da Ubangiji ku sa a karanta wannan wasiƙa ga dukan’yan’uwa.
28 The grace of our Lord Jesus Christ be with you. Amen.
Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku.

< 1 Thessalonians 5 >