< Psalms 26 >

1 By David. Judge me, LORD, for I have walked in my integrity. I have trusted also in the LORD without wavering.
Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
2 Examine me, LORD, and prove me. Try my heart and my mind.
Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
3 For your loving kindness is before my eyes. I have walked in your truth.
gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
4 I have not sat with deceitful men, neither will I go in with hypocrites.
Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
5 I hate the assembly of evildoers, and will not sit with the wicked.
na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
6 I will wash my hands in innocence, so I will go about your altar, LORD,
Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
7 that I may make the voice of thanksgiving to be heard and tell of all your wondrous deeds.
ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 LORD, I love the habitation of your house, the place where your glory dwells.
Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
9 Don’t gather my soul with sinners, nor my life with bloodthirsty men
Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
10 in whose hands is wickedness; their right hand is full of bribes.
waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
11 But as for me, I will walk in my integrity. Redeem me, and be merciful to me.
Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
12 My foot stands in an even place. In the congregations I will bless the LORD.
Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.

< Psalms 26 >