< Psalms 116 >

1 I love the LORD, because he listens to my voice, and my cries for mercy.
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Because he has turned his ear to me, therefore I will call on him as long as I live.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 The cords of death surrounded me, the pains of Sheol got a hold of me. I found trouble and sorrow. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
4 Then I called on the LORD’s name: “LORD, I beg you, deliver my soul.”
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 The LORD is gracious and righteous. Yes, our God is merciful.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 The LORD preserves the simple. I was brought low, and he saved me.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Return to your rest, my soul, for the LORD has dealt bountifully with you.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 For you have delivered my soul from death, my eyes from tears, and my feet from falling.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 I will walk before the LORD in the land of the living.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 I believed, therefore I said, “I was greatly afflicted.”
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 I said in my haste, “All people are liars.”
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 What will I give to the LORD for all his benefits towards me?
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 I will take the cup of salvation, and call on the LORD’s name.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 I will pay my vows to the LORD, yes, in the presence of all his people.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 Precious in the LORD’s sight is the death of his saints.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 LORD, truly I am your servant. I am your servant, the son of your servant girl. You have freed me from my chains.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 I will offer to you the sacrifice of thanksgiving, and will call on the LORD’s name.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 I will pay my vows to the LORD, yes, in the presence of all his people,
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 in the courts of the LORD’s house, in the middle of you, Jerusalem. Praise the LORD!
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalms 116 >