< Mark 1 >

1 The beginning of the Good News of Jesus Christ the Son of God.
Farkon bishara game da Yesu Kiristi, Ɗan Allah.
2 As it is written in Isaiah the Prophet, "See, I am sending My messenger before Thee, Who will prepare Thy way";
An rubuta a cikin littafin annabi Ishaya cewa, “Zan aika da ɗan aikena yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka,”
3 "The voice of one crying aloud: 'In the Desert prepare a road for the Lord: Make His highways straight.'"
“muryar mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 So John the Baptizer came, and was in the Desert proclaiming a baptism of the penitent for forgiveness of sins.
Ta haka Yohanna ya zo, yana baftisma a yankin hamada, yana kuma wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
5 There went out to him people of all classes from Judaea, and the inhabitants of Jerusalem of all ranks, and were baptized by him in the river Jordan, making open confession of their sins.
Dukan ƙauyukan Yahudiya da dukan mutanen Urushalima suka fiffito zuwa wurinsa. Suna furta zunubansu, ya kuwa yi musu baftisma a Kogin Urdun.
6 As for John, his garment was of camel's hair, and he wore a loincloth of leather; and his food was locusts and wild honey.
Yohanna ya sa tufafin gashin raƙumi, ya kuma yi ɗamara da fata. Abincinsa fāri ne da kuma zumar jeji.
7 His announcement was, "There is One coming after me mightier than I--One whose sandal-strap I am unworthy to stoop down and unfasten.
Wannan kuwa shi ne saƙonsa, “A bayana, wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban kuwa isa in sunkuya in kunce igiyar takalmansa ba.
8 I have baptized you with water, but He will baptize you with the Holy Spirit."
Ina muku baftisma da ruwa, amma shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
9 At that time Jesus came from Nazareth in Galilee and was baptized by John in the Jordan;
A lokacin, Yesu ya zo daga Nazaret na Galili, Yohanna kuwa ya yi masa baftisma a Urdun.
10 and immediately on His coming up out of the water He saw an opening in the sky, and the Spirit like a dove coming down to Him;
Da Yesu yana fitowa daga ruwan, sai ya ga sama ya buɗe, Ruhu kuma yana saukowa a kansa kamar kurciya.
11 and a voice came from the sky, saying, "Thou art My Son dearly loved: in Thee is My delight."
Sai murya ta fito daga sama ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, da kai kuma nake fari ciki ƙwarai.”
12 At once the Spirit impelled Him to go out into the Desert,
Nan da nan, sai Ruhu ya kai shi cikin hamada,
13 where He remained for forty days, tempted by Satan; and He was among the wild beasts, but the angels waited upon Him.
ya kuma kasance a hamada kwana arba’in, Shaiɗan yana gwada shi. Yana tare da namomin jeji, mala’iku kuma suka yi masa hidima.
14 Then, after John had been thrown into prison, Jesus came into Galilee proclaiming God's Good News.
Bayan da aka sa Yohanna a kurkuku, sai Yesu ya shigo cikin Galili, yana shelar bisharar Allah.
15 "The time has fully come," He said, "and the Kingdom of God is close at hand: repent, and believe this Good News.
Yana cewa, “Lokaci ya yi. Mulkin Allah ya yi kusa. Ku tuba, ku gaskata bishara!”
16 One day, passing along the shore of the Lake of Galilee, He saw Simon and Andrew, Simon's brother, throwing their nets in the Lake; for they were fisherman.
Yayinda Yesu yake tafiya a gaɓar Tekun Galili, sai ya ga Siman da ɗan’uwansa Andarawus, suna jefa abin kamun kifi a cikin tafkin, domin su masunta ne.
17 "Come and follow me," said Jesus, "and I will make you fishers for men."
Yesu ya ce, “Ku zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masuntan mutane.”
18 At once they left their nets and followed Him.
Nan da nan, suka bar abin kamun kifinsu, suka bi shi.
19 Going on a little further He saw James the son of Zabdi and his brother John: they also were in the boat mending the nets, and He immediately called them.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya ga Yaƙub ɗan Zebedi, da ɗan’uwansa Yohanna a cikin jirgin ruwa, suna gyaran abin kamun kifinsu.
20 They therefore left their father Zabdi in the boat with the hired men, and went and followed Him.
Ba da ɓata lokaci ba, ya kira su, sai suka bar mahaifinsu Zebedi a cikin jirgin ruwan, tare da’yan haya, suka kuwa bi shi.
21 So they came to Capernaum, and on the next Sabbath He went to the synagogue and began to teach.
Suka tafi Kafarnahum. Da ranar Asabbaci ta kewayo, sai Yesu ya shiga majami’a ya fara koyarwa.
22 The people listened with amazement to His teaching--for there was authority about it: it was very different from that of the Scribes--
Mutane suka yi mamakin koyarwarsa, domin ya koyar da su kamar wanda yake da iko, ba kamar malaman dokoki ba.
23 when all at once, there in their synagogue, a man under the power of a foul spirit screamed out:
Nan take, sai wani mutum mai mugun ruhu a majami’arsu, ya ɗaga murya ya ce,
24 "What have you to do with us, Jesus the Nazarene? Have you come to destroy us? I know who you are--God's Holy One."
“Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki nan na Allah!”
25 But Jesus reprimanded him, saying, "Silence! come out of him."
Yesu ya tsawata masa ya ce, “Yi shiru! Fita daga cikinsa!”
26 So the foul spirit, after throwing the man into convulsions, came out of him with a loud cry.
Sai mugun ruhun ya jijjiga mutumin da ƙarfi, ya fita daga jikinsa da ihu.
27 And all were amazed and awe-struck, so they began to ask one another, "What does this mean? Here is a new sort of teaching--and a tone of authority! And even to foul spirits he issues orders and they obey him!"
Dukan mutane suka yi mamaki, suna tambayar juna suna cewa, “Mene ne haka? Tabɗi! Yau ga sabuwar koyarwa kuma da iko! Yana ma ba wa mugayen ruhohi umarni, suna kuma yin masa biyayya.”
28 And His fame spread at once everywhere in all that part of Galilee.
Labari game da shi ya bazu nan da nan ko’ina a dukan yankin Galili.
29 Then on leaving the synagogue they came at once, with James and John, to the house of Simon and Andrew.
Da suka bar majami’ar, sai suka tafi gidan su Siman da Andarawus, tare da Yaƙub da Yohanna.
30 Now Simon's mother-in-law was ill in bed with a fever, and without delay they informed Him about her.
Surukar Siman tana kwance da zazzaɓi, sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 So He went to her, and taking her hand He raised her to her feet: the fever left her, and she began to wait upon them.
Sai ya je wajenta, ya kama hannunta, ya ɗaga ta. Zazzaɓin kuwa ya sāke ta, ta kuma yi musu hidima.
32 When it was evening, after sunset people came bringing Him all who were sick and the demoniacs;
A wannan yamma, bayan fāɗuwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan marasa lafiya, da masu aljanu.
33 and the whole town was assembled at the door.
Duk garin ya taru a ƙofar gidan.
34 Then He cured numbers of people who were ill with various diseases, and He drove out many demons; not allowing the demons to speak, because they knew who He was.
Yesu kuwa ya warkar da marasa lafiya da yawa da suke da cututtuka iri-iri. Ya kuma fitar da aljanu da yawa, amma bai yarda aljanun suka yi magana ba, don sun san wane ne shi.
35 In the morning He rose early, while it was still quite dark, and leaving the house He went away to a solitary place and there prayed.
Da sassafe, tun da sauran duhu, Yesu ya tashi, ya bar gida, ya tafi wani wurin da ba kowa, a can ya yi addu’a.
36 And Simon and the others searched everywhere for Him.
Siman da abokansa suka fita nemansa.
37 When they found Him they said, "Every one is looking for you."
Da suka same shi, sai suka ce, “Kowa yana nemanka!”
38 "Let us go elsewhere, to the neighbouring country towns," He replied, "that I may proclaim my Message there also; because for that purpose I came from God."
Yesu ya amsa ya ce, “Mu je wani wuri dabam, zuwa ƙauyukan da suke kusa, don in yi wa’azi a can ma. Wannan shi ne dalilin zuwana.”
39 And He went through all Galilee, preaching in the synagogues and expelling the demons.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
40 One day there came a leper to Jesus entreating Him, and pleading on his knees. "If you are willing," he said, "you are able to cleanse me."
Wani mutum mai kuturta ya zo wurinsa, ya durƙusa ya roƙe shi ya ce, “In kana so, za ka iya tsabtacce ni.”
41 Moved with pity Jesus reached out His hand and touched him. "I am willing," He said; "be cleansed."
Cike da tausayi, sai Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka tsabtacce!”
42 The leprosy at once left him, and he was cleansed.
Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi, ya kuma warke.
43 Jesus at once sent him away, strictly charging him,
Yesu ya sallame shi nan take, da gargaɗi mai ƙarfi cewa,
44 and saying, "Be careful not to tell any one, but go and show yourself to the Priest, and for your purification present the offerings that Moses appointed as evidence for them."
“Ka lura kada ka gaya wa kowa wannan. Amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayun da Musa ya umarta saboda tsarkakewarka, don yă zama shaida gare su.”
45 But the man, when he went out, began to tell every one and to publish the matter abroad, so that it was no longer possible for Jesus to go openly into any town; but He had to remain outside in unfrequented places, where people came to Him from all parts.
A maimakon haka, sai ya fita, ya fara magana a sake, yana baza labarin. Saboda haka, Yesu bai ƙara iya shiga cikin gari a fili ba, sai dai ya kasance a wuraren da ba kowa. Duk da haka, mutane suka yi ta zuwa wurinsa daga ko’ina.

< Mark 1 >