< Luke 5 >

1 On one occasion the crowd was pressing on Him and listening to God's Message, while He was standing by the Lake of Gennesaret.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 He, however, saw two fishing-boats drawn up on the beach (for the men had gone away from them and were washing the nets),
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 and going on board one of them, which was Simon's He asked him to push out a little from land. Then He sat down and taught the crowd of people from the boat.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 When He had finished speaking, He said to Simon, "Push out into deep water, and let down your nets for a haul."
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 "Rabbi," replied Peter, "all night long we have worked hard and caught nothing; but at your command I will let down the nets."
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 This they did, and enclosed a vast number of fish; and their nets began to break.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 So they signalled to their partners in the other boat to come and help them; they came, and they filled both the boats so that they almost sank.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 When Simon Peter saw this, he fell down at the knees of Jesus, and exclaimed, "Master, leave my boat, for I am a sinful man."
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 (For he was astonished and terrified--he and all his companions--at the haul of fish which they had taken;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 and so were Simon's partners James and John, the sons of Zabdi.) But Jesus replied to Simon, "Fear not: from this time you shall be a catcher of men."
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Then, after bringing their boats to land, they left everything and followed Him.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 On another occasion, when He was in one of the towns, there was a man there covered with leprosy, who, seeing Jesus, threw himself at His feet and implored Him, saying, "Sir, if only you are willing, you are able to make me clean."
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Reaching out His hand and touching him, Jesus said, "I am willing; be cleansed!" And instantly the leprosy left him.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 He ordered him to tell no one. "But go," He said, "show yourself to the Priest, and make the offering for your purification which Moses appointed, as evidence for them."
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 But all the more the report about Him spread abroad, and great multitudes crowded to hear Him and to be cured of their diseases;
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 but Jesus Himself constantly withdrew into the Desert and there prayed.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 One day He was teaching, and there were Pharisees and teachers of the Law sitting there who had come from every village in Galilee and Judaea and from Jerusalem. And the power of the Lord was present for Him to cure people.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 And a party of men came carrying a palsied man on a bed, and they endeavoured to bring him in and lay him before Jesus.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 But when they could find no way of doing so because of the crowd, they went up on the roof and let him down through the tiling--bed and all--into the midst, in front of Jesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 He saw their faith and said to him, "Friend, your sins are forgiven."
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Then the Scribes and Pharisees began to cavil, asking, "Who is this, uttering blasphemies? Who but God alone can forgive sins?"
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Well aware of their reasonings, Jesus answered their questions by asking in turn, "What is this that you are debating in your hearts?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Which is easier? --to say, 'Your sins are forgiven,' or to say, 'Rise and walk'?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 But to prove to you that the Son of Man has authority on earth to forgive sins" --Turning to the paralytic He said, "I bid you, Rise, take up your bed, and go home."
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Instantly he stood up in their presence, took up the mattress on which he had been lying, and went away to his home, giving glory to God.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Amazement seized them all. "Glory to God!" was the abiding feeling. Yet fear flashed through their minds and they said, "We have seen strange things to-day."
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 After this He went out and noticed a tax-gatherer, Levi by name, sitting at the Toll office; and He said to him, "Follow me."
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 He rose, left everything, and followed Him.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Levi also gave a great entertainment at his house in honour of Jesus, and there was a large party of tax-gatherers and others at table with them.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 This led the Pharisees and Scribes of their party to expostulate with His disciples and ask, "Why are you eating and drinking with these tax-gatherers and notorious sinners?"
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 But Jesus replied to them, "It is not men in good health who require a physician, but the sick.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I have not come to call the righteous to repentance, but sinners."
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Again they said to Him, "John's disciples fast often and pray, as do also those of the pharisees; but yours eat and drink."
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 "Can you compel the bridal party to fast," replied Jesus, "so long as they have the bridegroom among them?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 But a time for this will come, when the Bridegroom has been taken away from them: then, at that time, they will fast."
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 He also spoke in figurative language to them. "No one," He said, "tears a piece from a new garment to mend an old one. Otherwise he would not only spoil the new, but the patch from the new would not match the old.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Nor does any one pour new wine into old wine-skins. Otherwise the new wine would burst the skins, the wine itself would be spilt, and the skins be destroyed.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 But new wine must be put into fresh wineskins.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Nor does any one after drinking old wine wish for new; for he says, 'The old is better.'"
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luke 5 >