< Luke 17 >

1 Jesus said to His disciples, "It is inevitable that causes of stumbling should come; but alas for him through whom they come!
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 It would be well for him if, with a millstone round his neck, he were lying at the bottom of the sea, rather than that he should cause even one of these little ones to fall.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Be on your guard. "If your brother acts wrongly, reprove him; and if he is sorry, forgive him;
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 and if seven times in a day he acts wrongly towards you, and seven times turns again to you and says, 'I am sorry,' you must forgive him."
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 And the Apostles said to the Lord, "Give us faith."
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 "If your faith," replied the Lord, "is like a mustard seed, you might command this black-mulberry-tree, 'Tear up your roots and plant yourself in the sea,' and instantly it would obey you.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 But which of you who has a servant ploughing, or tending sheep, will say to him when he comes in from the farm, 'Come at once and take your place at table,'
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 and will not rather say to him, 'Get my dinner ready, make yourself tidy, and wait upon me till I have finished my dinner, and then you shall have yours'?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Does he thank the servant for obeying his orders?
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 So you also, when you have obeyed all the orders given you, must say, "'There is no merit in our service: what we have done is only what we were in duty bound to do.'"
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 As they pursued their journey to Jerusalem, He passed through Samaria and Galilee.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 And as He entered a certain village, ten men met Him who were lepers and stood at a distance.
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 In loud voices they cried out, "Jesus, Rabbi, take pity on us."
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 Perceiving this, He said to them, "Go and show yourselves to the Priests." And while on their way to do this they were made clean.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 One of them, seeing that he was cured, came back, adoring and praising God in a loud voice,
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 and he threw himself at the feet of Jesus, thanking Him. He was a Samaritan.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 "Were not all ten made clean?" Jesus asked; "but where are the nine?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 Have none been found to come back and give glory to God except this foreigner?"
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 And He said to him, "Rise and go: your faith has cured you."
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Being asked by the Pharisees when the Kingdom of God was coming, He answered, "The Kingdom of God does not so come that you can stealthily watch for it.
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 Nor will they say, 'See here!' or 'See there!' --for the Kingdom of God is within you."
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 Then, turning to His disciples, He said, "There will come a time when you will wish you could see a single one of the days of the Son of Man, but will not see one.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 And they will say to you, 'See there!' 'See here!' Do not start off and go in pursuit.
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 For just as the lightning, when it flashes, shines from one part of the horizon to the opposite part, so will the Son of Man be on His day.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 But first He must endure much suffering, and be rejected by the present generation.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 "And as it was in the time of Noah, so will it also be in the time of the Son of Man.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 Men were eating and drinking, taking wives and giving wives, up to the very day on which Noah entered the Ark, and the Deluge came and destroyed them all.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 The same was true in the time of Lot: they were eating and drinking, buying and selling, planting and building;
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 but on the day that Lot left Sodom, God rained fire and brimstone from the sky and destroyed them all.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Exactly so will it be on the day that the veil is lifted from the Son of Man.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 "On that day, if a man is on the roof and his property indoors, let him not go down to fetch it; and, in the same way, he who is in the field, let him not turn back.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Remember Lot's wife.
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Any man who makes it his object to keep his own life safe, will lose it; but whoever loses his life will preserve it.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 On that night, I tell you, there will be two men in one bed: one will be taken away and the other left behind.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 There will be two women turning the mill together: one will be taken away and the other left behind."
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 "Where, Master?" they inquired. "Where the dead body is," He replied, "there also will the vultures flock together."
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Luke 17 >