< Luke 1 >

1 Seeing that many have attempted to draw up a narrative of the facts which are received with full assurance among us
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 on the authority of those who were from the beginning eye-witnesses and were devoted to the service of the divine Message,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it has seemed right to me also, after careful investigation of the facts from their commencement, to write for you, most noble Theophilus, a connected account,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that you may fully know the truth of the things which you have been taught by word of mouth.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the time of Herod, the king of Judaea, a priest of the name of Zechariah, belonging to the class of Abijah. He had a wife who was a descendant of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were both of them upright before God, blamelessly obeying all the Lord's precepts and ordinances.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no child, because Elizabeth was barren; and both of them were far advanced in life.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Now while he was doing priestly duty before God in the prescribed course of his class,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 it fell to his lot--according to the custom of the priesthood--to go into the Sanctuary of the Lord and burn the incense;
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 and the whole multitude of the people were outside praying, at the hour of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Then there appeared to him an angel of the Lord standing on the right side of the altar of incense;
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 and Zechariah on seeing him was agitated and terrified.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, "Do not be afraid, Zechariah, for your petition has been heard: and your wife Elizabeth will bear you a son, and you are to call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Gladness and exultant joy shall be yours, and many will rejoice over his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord; no wine or fermented drink shall he ever drink; but he will be filled with the Holy Spirit from the very hour of his birth.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Many of the descendants of Israel will he turn to the Lord their God;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 and he will be His forerunner in the spirit and power of Elijah, to turn fathers' hearts to the children, and cause the rebellious to walk in the wisdom of the upright, to make a people perfectly ready for the lord."
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 "By what proof," asked Zechariah, "shall I know this? For I am an old man, and my wife is far advanced in years."
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 "I am Gabriel, who stand in the presence of God," answered the angel, "and I have been sent to talk with you and tell you this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And now you will be dumb and unable to speak until the day when this has taken place; because you did not believe my words--words which will be fulfilled at their appointed time."
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Meanwhile the people were waiting for Zechariah, and were surprised that he stayed so long in the Sanctuary.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 When, however, he came out, he was unable to speak to them; and they knew that he must have seen a vision in the Sanctuary; but he kept making signs to them and continued dumb.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 When his days of service were at an end, he went to his home;
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 and in course of time his wife Elizabeth conceived, and kept herself secluded five months.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 "Thus has the Lord dealt with me," she said, "now that He has graciously taken away my reproach among men."
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Now in the sixth month the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee called Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a maiden betrothed to a man of the name of Joseph, a descendant of David. The maiden's name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 So Gabriel went into the house and said to her, "Joy be to you, favoured one! the Lord is with you."
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 She was greatly agitated at his words, and wondered what such a greeting meant.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 But the angel said, "Do not be frightened, Mary, for you have found favour with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 You will conceive in your womb and bear a son; and you are to call His name JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great and He will be called 'Son of the Most High.' And the Lord God will give Him the throne of His forefather David;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and He will be King over the House of Jacob for the Ages, and of His Kingdom there will be no end." (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 "How can this be," Mary replied, "seeing that I have no husband?"
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 The angel answered, "The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will overshadow you; and for this reason your holy offspring will be called 'the Son of God.'
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And see, your relative Elizabeth--she also has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For no promise from God will be impossible of fulfilment."
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 "I am the Lord's maidservant," Mary replied; "may it be with me in accordance with your words!" And then the angel left her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Not long after this, Mary rose up and went in haste into the hill country to a town in Judah.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Here she came to the house of Zechariah and greeted Elizabeth;
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 and as soon as Elizabeth heard Mary's greeting, the babe leapt within her. And Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and uttered a loud cry of joy. "Blest among women are you," she said, "and the offspring of your body is blest!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 But why is this honour done me, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, the moment your greeting reached my ears, the babe within me leapt for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is she who has believed, for the word spoken to her from the Lord shall be fulfilled."
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Then Mary said: "My soul extols the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit triumphs in God my Saviour;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Because He has not turned from His maidservant in her lowly position; For from this time forward all generations will account me happy,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Because the mighty One has done great things for me--Holy is His name!--
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And His compassion is, generation after generation, Upon those who fear Him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He has manifested His supreme strength. He has scattered those who were haughty in the thoughts of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has cast monarchs down from their thrones, And exalted men of low estate.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 The hungry He has satisfied with choice gifts, But the rich He has sent empty-handed away.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 His servant Israel He has helped, Remembering His compassion--
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 In fulfillment of His promises to our forefathers--For Abraham and his posterity for ever." (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 So Mary stayed with Elizabeth about three months, and then returned home.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now when Elizabeth's full time was come, she gave birth to a son;
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 and her neighbours and relatives heard how the Lord had had great compassion on her; and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And on the eighth day they came to circumcise the child, and were going to call him Zechariah, after his father.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 His mother, however, said, "No, he is to be called John."
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 "There is not one of your family," they said, "who has that name."
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 They asked his father by signs what he wished him to be called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 So he asked for a writing-tablet, and wrote, "His name is John." And they all wondered.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Instantly his mouth and his tongue were set free, and he began to speak and bless God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And all who lived round about them were filled with awe, and throughout the hill country of Judaea reports of all these things were spread abroad.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 All who heard the story treasured it in their memories. "What then will this child be?" they said. For the lord's hand was indeed with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zechariah his father was filled with the Holy Spirit, and spoke in a rapture of praise.
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 "Blessed be the Lord, the God of Israel," he said, "Because He has not forgotten His people but has effected redemption for them,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And has raised up a mighty Deliverer for us In the house of David His servant--
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As He has spoken from all time by the lips of His holy Prophets-- (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 To deliver us from our foes and from the power of all who hate us.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 He dealt pitifully with our forefathers, And remembered His holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The oath which He swore to Abraham our forefather,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 To grant us to be rescued from the power of our foes And so render worship to Him free from fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 In piety and uprightness before Him all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you moreover, O child, shall be called Prophet of the Most High; For you shall go on in front before the Lord to prepare the way for Him,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To give to His People a knowledge of salvation In the forgiveness of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Through the tender compassion of our God, Through which the daybreak from on high will come to us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Dawning on those who now dwell in the darkness and shadow of death--To direct our feet into the path of peace."
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew and became strong in character, and lived in the Desert till the time came for him to appear publicly to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >