< Acts 3 >

1 One day Peter and John were going up to the Temple for the hour of prayer--the ninth hour--and, just then,
Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin addu’a da ƙarfe uku na rana.
2 some men were carrying there one who had been lame from birth, whom they were wont to place every day close to the Beautiful Gate (as it was called) of the Temple, for him to beg from the people as they went in.
To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don yă yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali.
3 Seeing Peter and John about to go into the Temple, he asked them for alms.
Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi.
4 Peter fixing his eyes on him, as John did also, said, "Look at us."
Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!”
5 So he looked and waited, expecting to receive something from them.
Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.
6 "I have no silver or gold," Peter said, "but what I have, I give you. In the name of Jesus Christ, the Nazarene-- walk!"
Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.”
7 Then taking his hand Peter lifted him up, and immediately his feet and ankles were strengthened.
Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi.
8 Leaping up, he stood upright and began to walk, and went into the Temple with them, walking, leaping, and praising God.
Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filin haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah.
9 All the people saw him walking and praising God;
Sa’ad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah,
10 and recognizing him as the man who used to sit at the Beautiful Gate of the Temple asking for alms, they were filled with awe and amazement at what had happened to him.
sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.
11 While he still clung to Peter and John, the people, awe-struck, ran up crowding round them in what was known as Solomon's Portico.
Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon.
12 Peter, seeing this, spoke to the people. "Israelites," he said, "why do you wonder at this man? Or why gaze at us, as though by any power or piety of our own we had enabled him to walk?
Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu, “Mutanen Isra’ila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke kallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya?
13 The God of Abraham, Isaac, and Jacob, the God of our forefathers, has conferred this honour on His Servant Jesus, whom you delivered up and disowned in the presence of Pilate, when he had decided to let Him go.
Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi.
14 Yes, you disowned the holy and righteous One, and asked as a favour the release of a murderer.
Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai.
15 The Prince of Life you put to death; but God has raised Him from the dead, and we are witnesses as to that.
Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan.
16 It is His name-- faith in that name being the condition--which has strengthened this man whom you behold and know; and the faith which He has given has made this man sound and strong again, as you can all see.
Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.
17 "And now, brethren, I know that it was in ignorance that you did it, as was the case with your rulers also.
“To,’yan’uwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi.
18 But in this way God has fulfilled the declarations He made through all the Prophets, that His Christ would suffer.
Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa cewa, Kiristinsa zai sha wahala.
19 Repent, therefore, and reform your lives, so that the record of your sins may be cancelled, and that there may come seasons of revival from the Lord,
Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokutan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji,
20 and that He may send the Christ appointed beforehand for you--even Jesus.
don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku, Yesu ke nan.
21 Heaven must receive Him until those times of which God has spoken from the earliest ages through the lips of His holy Prophets--the times of the reconstitution of all things. (aiōn g165)
Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn g165)
22 Moses declared, "'The Lord your God will raise up a Prophet for you from among your brethren as He has raised me. In all that He says to you, you must listen to Him.
Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku.
23 And every one, without exception, who refuses to listen to that Prophet shall be utterly destroyed from among the People.'
Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
24 Yes, and all the Prophets, from Samuel onwards--all who have spoken--have also announced the coming of this present time.
“Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki.
25 "You are the heirs of the Prophets, and of the Covenant which God made with your forefathers when He said to Abraham, 'And through your posterity all the families of the world shall be blessed.'
Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’
26 It is to you first that God, after raising His Servant from the grave, has sent Him to bless you, by causing every one of you to turn from your wickedness."
Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don yă albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”

< Acts 3 >