< Luke 18 >

1 And he spoke a parable to them [to this end], that men ought always [to] pray, and not to faint;
Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
2 Saying, There was in a city a judge, who feared not God, neither regarded man.
Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
3 And there was a widow in that city; and she came to him, saying, Avenge me of my adversary.
A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
4 And he would not for a while: but afterward he said within himself, Though I fear not God, nor regard man;
“An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
5 Yet because this widow troubleth me, I will avenge her, lest by her continual coming she weary me.
amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
6 And the Lord said, Hear what the unjust judge saith.
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
7 And will not God avenge his own elect, who cry day and night to him, though he beareth long with them?
Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
8 I tell you that he will avenge them speedily. Nevertheless, when the Son of man cometh, will he find faith on the earth?
Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
9 And he spoke this parable to certain who trusted in themselves that they were righteous, and despised others:
Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
10 Two men went up into the temple to pray; the one a Pharisee, and the other a publican.
“Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
11 The Pharisee stood and prayed thus with himself, God, I thank thee, that I am not as other men [are], extortioners, unjust, adulterers, or even as this publican.
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
12 I fast twice in the week, I give tithes of all that I possess.
Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
13 And the publican, standing afar off, would not lift up so much as [his] eyes to heaven, but smote upon his breast, saying, God be merciful to me a sinner.
“Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
14 I tell you, this man went down to his house justified [rather] than the other: for every one that exalteth himself shall be abased; and he that humbleth himself shall be exalted.
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
15 And they brought to him also infants, that he would touch them: but when [his] disciples saw [it], they rebuked them.
Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
16 But Jesus called them [to him], and said, Suffer little children to come to me, and forbid them not: for of such is the kingdom of God.
Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
17 Verily I say to you, Whoever shall not receive the kingdom of God as a little child, shall in no wise enter into it.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
18 And a certain ruler asked him, saying, Good Master, what shall I do to inherit eternal life? (aiōnios g166)
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
19 And Jesus said to him, Why callest thou me good? none [is] good, save one, [that is] God.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
20 Thou knowest the commandments, Do not commit adultery, Do not kill, Do not steal, Do not bear false witness, Honor thy father and thy mother.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
21 And he said, All these have I kept from my youth.
Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
22 Now when Jesus heard these things, he said to him, Yet lackest thou one thing: sell all that thou hast, and distribute to the poor, and thou shalt have treasure in heaven: and come, follow me.
Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
23 And when he heard this, he was very sorrowful: for he was very rich.
Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
24 And when Jesus saw that he was very sorrowful, he said, How hardly will they that have riches enter into the kingdom of God!
Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
25 For it is easier for a camel to go through a needle's eye, than for a rich man to enter into the kingdom of God.
Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 And they that heard [it], said, Who then can be saved?
Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
27 Then he said, The things which are impossible with men, are possible with God.
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
28 Then Peter said, Lo, we have left all, and followed thee.
Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
29 And he said to them, Verily I say to you, there is no man that hath left house, or parents, or brethren, or wife, or children for the sake of the kingdom of God,
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
30 Who shall not receive manifold more in this present time, and in the world to come life everlasting. (aiōn g165, aiōnios g166)
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Then he took the twelve, and said to them, Behold, we go up to Jerusalem, and all things that are written by the prophets concerning the Son of man shall be accomplished.
Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
32 For he will be delivered to the Gentiles, and will be mocked, and spitefully treated, and spitted on;
Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
33 And they will scourge [him], and put him to death: and the third day he will rise again.
za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
34 And they understood none of these things: and this saying was hid from them, neither knew they the things which were spoken.
Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
35 And it came to pass, that as he had come nigh to Jericho, a certain blind man sat by the way side begging;
Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
36 And hearing the multitude passing by, he asked what it meant.
Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
37 And they told him, that Jesus of Nazareth was passing by.
Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
38 And he cried, saying, Jesus, [thou] son of David, have mercy on me.
Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
39 And they who went before rebuked him, that he should hold his peace: but he cried so much the more, [Thou] son of David, have mercy on me.
Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
40 And Jesus stood and commanded him to be brought to him: and when he had come near, he asked him,
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
41 Saying, What wilt thou that I shall do to thee? And he said, Lord, that I may receive my sight.
“Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
42 And Jesus said to him, Receive thy sight: thy faith hath saved thee.
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 And immediately he received his sight, and followed him, glorifying God: and all the people, when they saw [it], gave praise to God.
Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.

< Luke 18 >