< Exodus 16 >

1 And they took their journey from Elim, and all the congregation of the children of Israel came to the wilderness of Sin, which [is] between Elim and Sinai, on the fifteenth day of the second month after their departure from the land of Egypt.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 And the whole congregation of the children of Israel murmured against Moses and Aaron in the wilderness.
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 And the children of Israel said to them, O that we had died by the hand of the LORD in the land of Egypt, when we sat by the flesh-pots, [and] when we did eat bread to the full: for ye have brought us forth into this wilderness, to kill this whole assembly with hunger.
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 Then said the LORD to Moses, Behold, I will rain bread from heaven for you; and the people shall go out and gather a certain rate every day, that I may prove them, whether they will walk in my law, or not.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 And it shall come to pass, that on the sixth day they shall prepare [that] which they bring in; and it shall be twice as much as they gather daily.
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 And Moses and Aaron said to all the children of Israel, At evening, then ye shall know that the LORD hath brought you out from the land of Egypt:
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 And in the morning, then ye shall see the glory of the LORD; for that he heareth your murmurings against the LORD: And what [are] we, that ye murmur against us?
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 And Moses said, [This shall be] when the LORD shall give you in the evening flesh to eat, and in the morning bread to the full; for that the LORD heareth your murmurings which ye murmur against him: And what [are] we? your murmurings [are] not against us, but against the LORD.
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 And Moses spoke to Aaron, Say to all the congregation of the children of Israel, Come near before the LORD: for he hath heard your murmurings.
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 And it came to pass, as Aaron spoke to the whole congregation of the children of Israel, that they looked towards the wilderness, and behold, the glory of the LORD appeared in the cloud.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 I have heard the murmurings of the children of Israel; Speak to them, saying, At evening ye shall eat flesh, and in the morning ye shall be filled with bread: and ye shall know that I [am] the LORD your God.
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 And it came to pass, that at evening the quails came up, and covered the camp: and in the morning the dew lay around the host.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 And when the dew that lay was gone up, behold, upon the face of the wilderness [there lay] a small round thing, [as] small as the hoar frost on the ground:
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 And when the children of Israel saw [it], they said one to another, It [is] manna: for they knew not what it [was]. And Moses said to them, This [is] the bread which the LORD hath given you to eat.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 This [is] the thing which the LORD hath commanded, Gather of it every man according to his eating: an omer for every man [according to] the number of your persons, take ye every man for [them] who [are] in his tents.
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 And the children of Israel did so, and gathered, some more, some less.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 And when they measured [it] with an omer, he that gathered much had nothing over, and he that gathered little had no lack: they gathered every man according to his eating.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 And Moses said, Let no man leave of it till the morning.
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 Notwithstanding, they hearkened not to Moses; but some of them left of it until the morning, and it bred worms, and became offensive; and Moses was wroth with them.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 And they gathered it every morning, every man according to his eating: and when the sun became hot, it melted.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 And it came to pass, [that] on the sixth day they gathered twice as much bread, two omers for one [man]: and all the rulers of the congregation came and told Moses.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 And he said to them, This [is that] which the LORD hath said, To-morrow [is] the rest of the holy sabbath to the LORD: bake [that] which ye will bake [to-day], and boil that ye will boil; and that which remaineth over, lay up for you to be kept until the morning.
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 And they laid it up till the morning, as Moses ordered: and it did not putrefy, neither was there any worm therein.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 And Moses said, Eat that to-day; for to-day [is] a sabbath to the LORD; to-day ye will not find it in the field.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Six days ye shall gather it; but on the seventh day, [which is] the sabbath, in it there will be none.
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 And it came to pass, [that some] of the people went out on the seventh day to gather, and they found none.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 And the LORD said to Moses, How long refuse ye to keep my commandments and my laws?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 See, for that the LORD hath given you the sabbath, therefore he giveth you on the sixth day the bread of two days: abide ye every man in his place, let no man go out of his place on the seventh day.
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 So the people rested on the seventh day.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 And the house of Israel called its name Manna: and it [was] like coriander-seed, white; and the taste of it [was] like wafers [made] with honey.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 And Moses said, This [is] the thing which the LORD commanded, Fill an omer of it to be kept for your generations; that they may see the bread with which I fed you in the wilderness, when I brought you forth from the land of Egypt.
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 And Moses said to Aaron, Take a pot, and put an omer full of manna therein, and lay it up before the LORD, to be kept for your generations.
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 As the LORD commanded Moses, so Aaron laid it up before the Testimony, to be kept.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 And the children of Israel ate manna forty years, until they came to a land inhabited: they ate manna, until they came to the borders of the land of Canaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 Now an omer [is] the tenth [part] of an ephah.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exodus 16 >