< Romans 14 >

1 Him that is weak in the faith receive ye, but not to doubtful disputations.
Ku karbi duk wanda yake da rarraunar bangaskiya, ba tare da sukar ra'ayinsa ba.
2 For one believeth that he may eat all things: another, who is weak, eateth herbs.
Wani yana da bangaskiyar yaci komai, wani wanda yake da rauni yakanci ganye ne kawai.
3 Let not him that eateth despise him that eateth not; and let not him who eateth not judge him that eateth: for God hath received him.
Kada wanda yake cin komai ya raina wanda baya cin kowanne abu. Kada kuma wanda baya cin kowanne abu ya shara'anta sauran da suke cin komai. Saboda Allah ya karbe shi.
4 Who art thou that judgest another man’s servant? to his own master he standeth or falleth. And, he shall be held up: for God is able to make him stand.
Kai wanene, kai wanene da kake ganin laifin bawan wani? Tsayawarsa ko faduwarsa ai hakin maigidansa ne, amma Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5 One man esteemeth one day above another: another esteemeth every day alike. Let every man be fully persuaded in his own mind.
Wani yakan daukaka wata rana fiye da sauran. Wani kuma yana daukan ranakun daidai. Kowa ya zauna a cikin hakakkewa akan ra'ayinsa.
6 He that regardeth the day, regardeth it to the Lord; and he that regardeth not the day, to the Lord he doth not regard it. He that eateth, eateth to the Lord, for he giveth God thanks; and he that eateth not, to the Lord he eateth not, and giveth God thanks.
Shi wanda ya kula da wata rana, ya kula da ita don Ubangiji. Kuma wanda yaci, yaci ne domin Ubangiji, domin yana yi wa Allah godiya. Shi wanda bai ci ba, yaki ci ne domin Ubangiji. Shima yana yi wa Allah godiya.
7 For none of us liveth to himself, and no man dieth to himself.
Domin babu wanda yake rayuwa don kansa a cikinmu, kuma babu mai mutuwa don kansa.
8 For whether we live, we live to the Lord; and whether we die, we die to the Lord: whether we live therefore, or die, we are the Lord’s.
Domin in muna raye, muna raye don Ubangiji. Kuma in mun mutu, mun mutu ne don Ubangiji. Ashe, ko muna raye, ko a mace mu na Ubangiji ne.
9 For to this end Christ both died, and rose, and revived, that he might be Lord both of the dead and the living.
Domin wannan dalilin Almasihu ya mutu ya kuma tashi, saboda ya zama Ubangiji ga matattu da rayayyu.
10 But why dost thou judge thy brother? or why dost thou show contempt for thy brother? for we shall all stand before the judgment seat of Christ.
Amma ku don me kuke shara'anta yan'uwanku? kai kuma don me kake raina dan'uwanka? Dukan mu zamu tsaya gaban kursiyin shari'ar Allah.
11 For it is written, As I live, saith the Lord, every knee shall bow to me, and every tongue shall confess to God.
Domin a rubuce yake, “Na rantse, “inji Ubangiji”, kowacce gwiwa zata rusuna mani, kowanne harshe kuwa zai yabi Allah.”
12 So then every one of us shall give account of himself to God.
Domin kowannenmu zai fadi abin da shi yayi da bakinsa a gaban Allah.
13 Let us not therefore judge one another any more: but judge this rather, that no man put a stumblingblock or an occasion to fall in his brother’s way.
Saboda da haka kada muyi wa juna shari'a, amma maimakon haka ku dauki wannan kudduri, don kada kowa ya zama sanadin tuntunbe ko faduwa ga dan'uwansa.
14 I know, and am persuaded by the Lord Jesus, that there is nothing unclean by itself: but to him that esteemeth any thing to be unclean, to him it is unclean.
Na sani na kuma tabbata tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake mara tsarki ga asalinsa. Sai dai ga wanda ya dauke shi marar tsarki ne yake zama marar tsarki.
15 But if thy brother is grieved with thy food, now walkest thou not in love. Destroy not him with thy food, for whom Christ died.
Idan har abincinka na cutar da dan'uwanka, ba ka tafiya cikin kauna. Kada ka lalata wanda Yesu ya mutu domin sa da abincinka.
16 Let not then your good be evil spoken of:
Saboda haka, kada abubuwan da aka dauka kyawawa su zama abin zargi ga wadansu.
17 For the kingdom of God is not food and drink; but righteousness, and peace, and joy in the Holy Spirit.
Saboda mulkin Allah ba maganar ci da sha ba ne, amma game da adalci ne, salama, da farin ciki a cikin Ruhu Mai Tsarki.
18 For he that in these things serveth Christ is acceptable to God, and approved by men.
Domin wanda yake bautar Almasihu a wannan hanya, karbabbe ne ga Allah, kuma jama'a sun yarda da shi.
19 Let us therefore follow after the things which make for peace, and things which one may edify another.
Don haka, mu nemi abubuwa na salama da abubuwan da zasu gina juna.
20 For the sake of food destroy not the work of God. All things indeed are pure; but it is evil for that man who eateth with offence.
Kada ku lalata aikin Allah don abinci. Komai yana da tsarki, amma kaiton mutumin da yake cin abin da zai sa shi ya fadi.
21 It is good neither to eat flesh, nor to drink wine, nor any thing by which thy brother stumbleth, or is offended, or is made weak.
Bashi da kyau a ci nama ko a sha ruwan inabi, ko duk abin da zai jawo faduwar dan'uwanka.
22 Hast thou faith? have it to thyself before God. Happy is he that condemneth not himself in what he approveth.
Wannan bangaskiyar da kuke da ita, ku adana ta tsakaninku da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa bata da laifi akan abin da hankalinsa ya ga daidai ne.
23 And he that doubteth is condemned if he eateth, because he eateth not from faith: for whatever is not from faith is sin.
Duk wanda yayi shakka amma kuma yaci, ya sani yayi laifi kenan, domin ba tare da bangaskiya bane. Duk abin da ba na bangaskya bane zunubi ne.

< Romans 14 >