< Psalms 22 >

1 To the chief Musician upon Aijeleth Shahar, A Psalm of David. My God, my God, why hast thou forsaken me? why art thou so far from helping me, and from the words of my roaring?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 O my God, I cry in the daytime, but thou hearest not; and in the night season, and am not silent.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 But thou art holy, O thou that inhabitest the praises of Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Our fathers trusted in thee: they trusted, and thou didst deliver them.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 They cried to thee, and were delivered: they trusted in thee, and were not confounded.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 But I am a worm, and no man; a reproach of men, and despised by the people.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 All they that see me mock me: they shoot out the lip, they shake the head, saying,
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 He trusted on the LORD that he would deliver him: let him deliver him, seeing he delighted in him.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 But thou art he that brought me out of the womb: thou didst make me hope when I was upon my mother’s breasts.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 I was cast upon thee from my birth: thou art my God from my mother’s womb.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Be not far from me; for trouble is near; for there is none to help.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Many bulls have surrounded me: strong bulls of Bashan have beset me all round.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 They gaped upon me with their mouths, as a ravening and a roaring lion.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 I am poured out like water, and all my bones are out of joint: my heart is like wax; it is melted within me.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 My strength is dried up like a potsherd; and my tongue cleaveth to my jaws; and thou hast brought me into the dust of death.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 For dogs have surrounded me: the assembly of the wicked have inclosed me: they pierced my hands and my feet.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 I may number all my bones: they look and stare upon me.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 They part my garments among them, and cast lots upon my vesture.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 But be not thou far from me, O LORD: O my strength, haste thee to help me.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Deliver my soul from the sword; my darling from the power of the dog.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Save me from the lion’s mouth: for thou hast heard me from the horns of the unicorns.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 I will declare thy name to my brethren: in the midst of the congregation will I praise thee.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Ye that fear the LORD, praise him; all ye the seed of Jacob, glorify him; and fear him, all ye the seed of Israel.
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 For he hath not despised nor abhorred the affliction of the afflicted; neither hath he hid his face from him; but when he cried to him, he heard.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 My praise shall be of thee in the great congregation: I will pay my vows before them that fear him.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 The meek shall eat and be satisfied: they shall praise the LORD that seek him: your heart shall live for ever.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 All the ends of the world shall remember and turn to the LORD: and all the kindreds of the nations shall worship before thee.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 For the kingdom is the LORD’S: and he is the governor among the nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 All the prosperous of the earth shall eat and worship: all they that go down to the dust shall bow before him: and none can keep alive his own soul.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 A seed shall serve him; it shall be accounted to the Lord for a generation.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 They shall come, and shall declare his righteousness to a people that shall be born, that he hath done this.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Psalms 22 >