< Psalms 106 >

1 Praise ye the LORD. O give thanks to the LORD; for he is good: for his mercy endureth for ever.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Who can utter the mighty acts of the LORD? who can show forth all his praise?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Blessed are they that keep judgment, and he that doeth righteousness at all times.
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Remember me, O LORD, with the favour that thou bearest to thy people: O visit me with thy salvation;
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 That I may see the good of thy chosen, that I may rejoice in the gladness of thy nation, that I may glory with thy inheritance.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 We have sinned with our fathers, we have committed iniquity, we have done wickedly.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Our fathers understood not thy wonders in Egypt; they remembered not the multitude of thy mercies; but provoked him at the sea, even at the Red sea.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Nevertheless he saved them for his name’s sake, that he might make his mighty power to be known.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 He rebuked the Red sea also, and it was dried up: so he led them through the depths, as through the wilderness.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 And he saved them from the hand of him that hated them, and redeemed them from the hand of the enemy.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 And the waters covered their enemies: there was not one of them left.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Then they believed his words; they sang his praise.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 They soon forgot his works; they waited not for his counsel:
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 But lusted exceedingly in the wilderness, and tempted God in the desert.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 And he gave them their request; but sent leanness into their soul.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 They envied Moses also in the camp, and Aaron the saint of the LORD.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 The earth opened and swallowed up Dathan, and covered the company of Abiram.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 And a fire was kindled in their company; the flame burned up the wicked.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 They made a calf in Horeb, and worshipped the molten image.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Thus they changed their glory into the similitude of an ox that eateth grass.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 They forgot God their saviour, who had done great things in Egypt;
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Wondrous works in the land of Ham, and terrible things by the Red sea.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Therefore he said that he would destroy them, had not Moses his chosen stood before him in the breach, to turn away his wrath, lest he should destroy them.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Yea, they despised the pleasant land, they believed not his word:
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 But murmured in their tents, and hearkened not to the voice of the LORD.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Therefore he lifted up his hand against them, to overthrow them in the wilderness:
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 To overthrow their seed also among the nations, and to scatter them in the lands.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 They joined themselves also to Baalpeor, and ate the sacrifices of the dead.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Thus they provoked him to anger with their deeds: and the plague broke in upon them.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Then stood up Phinehas, and executed judgment: and so the plague was stopped.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 And that was counted to him for righteousness to all generations for evermore.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 They angered him also at the waters of strife, so that it went ill with Moses for their sakes:
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Because they provoked his spirit, so that he spoke unadvisedly with his lips.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 They did not destroy the nations, concerning whom the LORD commanded them:
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 But were mingled among the heathen, and learned their works.
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 And they served their idols: which were a snare to them.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Yea, they sacrificed their sons and their daughters to demons,
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 And shed innocent blood, even the blood of their sons and of their daughters, whom they sacrificed to the idols of Canaan: and the land was polluted with blood.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Thus were they defiled with their own works, and went astray with their own deeds.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Therefore was the wrath of the LORD kindled against his people, insomuch that he abhorred his own inheritance.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 And he gave them into the hand of the heathen; and they that hated them ruled over them.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Their enemies also oppressed them, and they were brought into subjection under their hand.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Many times did he deliver them; but they provoked him with their counsel, and were brought low for their iniquity.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Nevertheless he regarded their affliction, when he heard their cry:
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 And he remembered for them his covenant, and repented according to the multitude of his mercies.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 He made them also to be pitied by all those that carried them captives.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Save us, O LORD our God, and gather us from among the heathen, to give thanks to thy holy name, and to triumph in thy praise.
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Blessed be the LORD God of Israel from everlasting to everlasting: and let all the people say, Amen. Praise ye the LORD.
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psalms 106 >