< Luke 13 >

1 There were present at that season some that told him of the Galilaeans, whose blood Pilate had mingled with their sacrifices.
A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
2 And Jesus answering said to them, Suppose ye that these Galilaeans were sinners above all the Galilaeans, because they suffered such things?
Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
3 I tell you, Nay: but, except ye repent, ye shall all likewise perish.
A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
4 Or those eighteen, upon whom the tower in Siloam fell, and killed them, think ye that they were sinners above all men that dwelt in Jerusalem?
Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
5 I tell you, Nay: but, except ye repent, ye shall all likewise perish.
Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
6 He spoke also this parable; A certain man had a fig tree planted in his vineyard; and he came and sought fruit on it, and found none.
Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
7 Then said he to the dresser of his vineyard, Behold, these three years I come seeking fruit on this fig tree, and find none: cut it down; why cumbereth it the ground?
Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
8 And he answering said to him, Lord, let it alone this year also, till I shall dig about it, and dung it:
Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
9 And if it shall bear fruit, well: and if not, then after that thou shalt cut it down.
In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
10 And he was teaching in one of the synagogues on the sabbath.
Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
11 And, behold, there was a woman who had a spirit of infirmity eighteen years, and was bowed together, and could in no way raise herself.
Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
12 And when Jesus saw her, he called her to him, and said to her, Woman, thou art loosed from thy infirmity.
Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
13 And he laid his hands on her: and immediately she was made straight, and glorified God.
Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
14 And the ruler of the synagogue answered with indignation, because Jesus had healed on the sabbath, and said to the people, There are six days in which men ought to work: in them therefore come and be healed, and not on the sabbath day.
Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
15 The Lord then answered him, and said, Thou hypocrite, doth not each one of you on the sabbath loose his ox or his donkey from the stall, and lead him away to watering?
Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
16 And ought not this woman, being a daughter of Abraham, whom Satan hath bound, lo, these eighteen years, to be loosed from this bond on the sabbath day?
Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
17 And when he had said these things, all his adversaries were ashamed: and all the people rejoiced for all the glorious things that were done by him.
Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
18 Then said he, To what is the kingdom of God like? and to what shall I compare it?
Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
19 It is like a grain of mustard seed, which a man took, and cast into his garden; and it grew, and became a great tree; and the fowls of the air lodged in its branches.
Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
20 And again he said, To what shall I liken the kingdom of God?
Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
21 It is like leaven, which a woman took and hid in three measures of meal, till the whole was leavened.
Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
22 And he went through the cities and villages, teaching, and journeying toward Jerusalem.
Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
23 Then said one to him, Lord, are there few that are saved? And he said to them,
Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
24 Strive to enter in at the narrow gate: for many, I say to you, will seek to enter in, and shall not be able.
“Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
25 When once the master of the house hath risen up, and hath shut the door, and ye begin to stand without, and to knock at the door, saying, Lord, Lord, open to us; and he shall answer and say to you, I know you not where ye are from:
In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
26 Then ye shall begin to say, We ate and drank in thy presence, and thou hast taught in our streets.
Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
27 But he shall say, I tell you, I know you not where ye are from; depart from me, all ye workers of iniquity.
Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
28 There shall be weeping and gnashing of teeth, when ye shall see Abraham, and Isaac, and Jacob, and all the prophets, in the kingdom of God, and you yourselves thrust out.
Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
29 And they shall come from the east, and from the west, and from the north, and from the south, and shall sit down in the kingdom of God.
Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
30 And, behold, there are last who shall be first, and there are first who shall be last.
Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
31 The same day there came certain of the Pharisees, saying to him, Go away, and depart from here: for Herod will kill thee.
Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
32 And he said to them, Go ye, and tell that fox, Behold, I cast out demons, and I do cures to day and to morrow, and the third day I shall be perfected.
Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
33 Nevertheless I must walk to day, and to morrow, and the day following: for it cannot be that a prophet should perish out of Jerusalem.
Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
34 O Jerusalem, Jerusalem, that killest the prophets, and stonest them that are sent to thee; how often would I have gathered thy children together, as a hen gathereth her brood under her wings, and ye would not!
Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
35 Behold, your house is left to you desolate: and verily I say to you, Ye shall not see me, until the time shall come when ye shall say, Blessed is he that cometh in the name of the Lord.
Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”

< Luke 13 >