< Luke 1 >

1 Forasmuch as many have taken in hand to set forth in order a declaration of those things which are most surely believed among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Even as they delivered them to us, who from the beginning were eyewitnesses, and ministers of the word;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 It seemed good to me also, having had perfect understanding of all things from the very first, to write to thee in order, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 That thou mayest know the certainty of those things, in which thou hast been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod, the king of Judaea, a certain priest named Zacharias, of the course of Abijah: and his wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And they were both righteous before God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord blameless.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no child, because Elisabeth was barren, and they both were well advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to pass, that while he executed the priest’s office before God in the order of his course,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 According to the custom of the priest’s office, his lot was to burn incense when he went into the temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And the whole multitude of the people were praying outside at the time of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him an angel of the Lord standing on the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And when Zacharias saw him, he was troubled, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, Fear not, Zacharias: for thy prayer is heard; and thy wife Elisabeth shall bear thee a son, and thou shalt call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And thou shalt have joy and gladness; and many shall rejoice at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he shall be great in the sight of the Lord, and shall drink neither wine nor strong drink; and he shall be filled with the Holy Spirit, even from his mother’s womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And many of the children of Israel shall he turn to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he shall go before him in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of the fathers to the children, and the disobedient to the wisdom of the just; to make ready a people prepared for the Lord.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said to the angel, How shall I know this? for I am an old man, and my wife well advanced in years.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel answering said to him, I am Gabriel, who stand in the presence of God; and am sent to speak to thee, and to show thee these glad tidings.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And, behold, thou shalt be dumb, and not able to speak, until the day that these things shall be performed, because thou believest not my words, which shall be fulfilled in their season.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people waited for Zacharias, and marvelled that he tarried so long in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And when he came out, he could not speak to them: and they perceived that he had seen a vision in the temple: for he made signs to them, and remained speechless.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, that, as soon as the days of his ministration were accomplished, he departed to his own house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after those days his wife Elisabeth conceived, and hid herself five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus hath the Lord dealt with me in the days when he looked on me, to take away my reproach among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 And in the sixth month the angel Gabriel was sent from God to a city of Galilee, named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 To a virgin espoused to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the virgin’s name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the angel came to her, and said, Hail, thou that art highly favoured, the Lord is with thee: blessed art thou among women.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And when she saw him, she was troubled at his saying, and considered in her mind what manner of greeting this should be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said to her, Fear not, Mary: for thou hast found favour with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And, behold, thou shalt conceive in thy womb, and bring forth a son, and shalt call his name JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Highest: and the Lord God shall give to him the throne of his father David:
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 And he shall reign over the house of Jacob for ever; and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Then said Mary to the angel, How shall this be, seeing I know not a man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the angel answered and said to her, The Holy Spirit shall come upon thee, and the power of the Highest shall overshadow thee: therefore also that holy thing who shall be born of thee shall be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And, behold, thy cousin Elisabeth, hath also conceived a son in her old age: and this is the sixth month with her, who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For with God nothing shall be impossible.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said, Behold the handmaid of the Lord; be it to me according to thy word. And the angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Mary arose in those days, and went into the hill country with haste, into a city of Judah;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 And entered into the house of Zacharias, and greeted Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, that, when Elisabeth heard the greeting of Mary, the babe leaped in her womb; and Elisabeth was filled with the Holy Spirit:
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 And she spoke with a loud voice, and said, Blessed art thou among women, and blessed is the fruit of thy womb.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And why is this granted to me, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, lo, as soon as the voice of thy greeting sounded in my ears, the babe leaped in my womb for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is she that believed: that there shall be a performance of those things which were told her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, My soul doth magnify the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit hath rejoiced in God my Saviour.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 For he hath regarded the low estate of his handmaiden: for, behold, from henceforth all generations shall call me blessed.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For he that is mighty hath done to me great things; and holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is on them that fear him from generation to generation.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He hath shown strength with his arm; he hath scattered the proud in the imagination of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He hath put down the mighty from their seats, and exalted them of low degree.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He hath filled the hungry with good things; and the rich he hath sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He hath helped his servant Israel, in remembrance of his mercy;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 As he spoke to our fathers, to Abraham, and to his seed for ever. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary abode with her about three months, and returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now Elisabeth’s full time came that she should be delivered; and she brought forth a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbours and her cousins heard that the Lord had shown great mercy upon her; and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass, that on the eighth day they came to circumcise the child; and they called him Zacharias, after the name of his father.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother answered and said, Not so; but he shall be called John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, There is none of thy kindred that is called by this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, how he would have him called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And he asked for a writing tablet, and wrote, saying, His name is John. And they all marvelled.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And his mouth was opened immediately, and his tongue loosed, and he spoke, and praised God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came on all that dwelt around them: and all these sayings were noised abroad throughout all the hill country of Judaea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all they that had heard them laid them up in their hearts, saying, What manner of child shall this be! And the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And his father Zacharias was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed be the Lord God of Israel; for he hath visited and redeemed his people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And hath raised up an horn of salvation for us in the house of his servant David;
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As he spoke by the mouth of his holy prophets, who have been since the world began: (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 That we should be saved from our enemies, and from the hand of all that hate us;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To perform the mercy promised to our fathers, and to remember his holy covenant;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The oath which he swore to our father Abraham,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 That he would grant to us, that we being delivered out of the hand of our enemies might serve him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 In holiness and righteousness before him, all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, shalt be called the prophet of the Highest: for thou shalt go before the face of the Lord to prepare his ways;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To give knowledge of salvation to his people by the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Through the tender mercy of our God; with which the dayspring from on high hath visited us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To give light to them that sit in darkness and in the shadow of death, to guide our feet into the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and became strong in spirit, and was in the deserts till the day of his showing to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >