< Joshua 13 >

1 Now Joshua was old and advanced in years; and the LORD said to him, Thou art old and advanced in years, and there remaineth yet very much land to be possessed.
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 This is the land that yet remaineth: all the borders of the Philistines, and all Geshuri,
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 From Sihor, which is before Egypt, even to the borders of Ekron northward, which is counted to the Canaanite: five lords of the Philistines; the Gazathites, and the Ashdothites, the Eshkalonites, the Gittites, and the Ekronites; also the Avites:
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 From the south, all the land of the Canaanites, and Mearah that is beside the Sidonians, to Aphek, to the borders of the Amorites:
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 And the land of the Giblites, and all Lebanon, toward the sunrising, from Baalgad under mount Hermon to the entrance into Hamath.
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 And the inhabitants of the hill country from Lebanon to Misrephothmaim, and all the Sidonians, them will I drive out from before the children of Israel: only divide thou it by lot to the Israelites for an inheritance, as I have commanded thee.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 Now therefore divide this land for an inheritance to the nine tribes, and the half tribe of Manasseh,
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 With whom the Reubenites and the Gadites have received their inheritance, which Moses gave them, beyond Jordan eastward, even as Moses the servant of the LORD gave them;
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 From Aroer, that is upon the bank of the river Arnon, and the city that is in the midst of the river, and all the plain of Medeba to Dibon;
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 And all the cities of Sihon king of the Amorites, who reigned in Heshbon, to the border of the children of Ammon;
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 And Gilead, and the border of the Geshurites and Maachathites, and all mount Hermon, and all Bashan to Salcah;
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 All the kingdom of Og in Bashan, who reigned in Ashtaroth and in Edrei, who remained of the remnant of the giants: for these did Moses smite, and cast them out.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 Nevertheless the children of Israel drove not out the Geshurites, nor the Maachathites: but the Geshurites and the Maachathites dwell among the Israelites until this day.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 Only to the tribe of Levi he gave no inheritance; the sacrifices of the LORD God of Israel made by fire are their inheritance, as he said to them.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 And Moses gave to the tribe of the children of Reuben inheritance according to their families.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 And their land was from Aroer, that is on the bank of the river Arnon, and the city that is in the midst of the river, and all the plain by Medeba;
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 Heshbon, and all its cities that are in the plain; Dibon, and Bamothbaal, and Bethbaalmeon,
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 And Jahazah, and Kedemoth, and Mephaath,
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 And Kirjathaim, and Sibmah, and Zarethshahar in the mount of the valley,
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 And Bethpeor, and Ashdothpisgah, and Bethjeshimoth,
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 And all the cities of the plain, and all the kingdom of Sihon king of the Amorites, who reigned in Heshbon, whom Moses smote with the princes of Midian, Evi, and Rekem, and Zur, and Hur, and Reba, who were chiefs of Sihon, dwelling in the country.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 Balaam also the son of Beor, the soothsayer, did the children of Israel slay with the sword among them that were slain by them.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 And the border of the children of Reuben was Jordan, and its border. This was the inheritance of the children of Reuben after their families, the cities and their villages.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 And Moses gave inheritance to the tribe of Gad, even to the children of Gad according to their families.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 And their land was Jazer, and all the cities of Gilead, and half the land of the children of Ammon, to Aroer that is before Rabbah;
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 And from Heshbon to Ramathmizpeh, and Betonim; and from Mahanaim to the border of Debir;
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 And in the valley, Betharam, and Bethnimrah, and Succoth, and Zaphon, the rest of the kingdom of Sihon king of Heshbon, Jordan and its border, even to the edge of the sea of Chinnereth on the other side of Jordan eastward.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 This is the inheritance of the children of Gad after their families, the cities, and their villages.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 And Moses gave inheritance to the half tribe of Manasseh: and this was the possession of the half tribe of the children of Manasseh by their families.
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 And their land was from Mahanaim, all Bashan, all the kingdom of Og king of Bashan, and all the towns of Jair, which are in Bashan, sixty cities:
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 And half Gilead, and Ashtaroth, and Edrei, cities of the kingdom of Og in Bashan, went to the children of Machir the son of Manasseh, even to the one half of the children of Machir by their families.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 These are the countries which Moses distributed for inheritance in the plains of Moab, on the other side of Jordan, by Jericho, eastward.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 But to the tribe of Levi Moses gave not any inheritance: the LORD God of Israel was their inheritance, as he said to them.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Joshua 13 >