< John 15 >

1 I am the true vine, and my Father is the vinedresser.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 Every branch in me that beareth not fruit he taketh away: and every branch that beareth fruit, he trimmeth it, that it may bring forth more fruit.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 Now ye are clean through the word which I have spoken to you.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Abide in me, and I in you. As the branch cannot bear fruit of itself, except it abide in the vine; no more can ye, except ye abide in me.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 I am the vine, ye are the branches: He that abideth in me, and I in him, the same bringeth forth much fruit: for without me ye can do nothing.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 If a man abideth not in me, he is cast forth as a branch, and is withered; and men gather them, and cast them into the fire, and they are burned.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 If ye abide in me, and my words abide in you, ye shall ask what ye will, and it shall be done to you.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 In this is my Father glorified, that ye bear much fruit; so shall ye be my disciples.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 As the Father hath loved me, so have I loved you: continue ye in my love.
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 If ye keep my commandments, ye shall abide in my love; even as I have kept my Father’s commandments, and abide in his love.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 These things have I spoken to you, that my joy may remain in you, and that your joy may be full.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 This is my commandment, That ye love one another, as I have loved you.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 Greater love hath no man than this, that a man lay down his life for his friends.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 Ye are my friends, if ye do whatever I command you.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 Henceforth I call you not servants; for the servant knoweth not what his lord doeth: but I have called you friends; for all things that I have heard from my Father I have made known to you.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 Ye have not chosen me, but I have chosen you, and ordained you, that ye should go and bring forth fruit, and that your fruit should remain: that whatever ye shall ask of the Father in my name, he may give it to you.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 These things I command you, that ye love one another.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 If the world hateth you, ye know that it hated me before it hated you.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 If ye were of the world, the world would love its own: but because ye are not of the world, but I have chosen you out of the world, therefore the world hateth you.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Remember the word that I said to you, The servant is not greater than his lord. If they have persecuted me, they will also persecute you; if they have kept my saying, they will keep yours also.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 But all these things will they do to you for my name’s sake, because they know not him that sent me.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 If I had not come and spoken to them, they had not had sin: but now they have no cloke for their sin.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 He that hateth me hateth my Father also.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 If I had not done among them the works which no other man hath done, they had not had sin: but now have they both seen and hated both me and my Father.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 But this cometh to pass, that the word might be fulfilled that is written in their law, They hated me without a cause.
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 But when the Comforter is come, whom I will send to you from the Father, even the Spirit of truth, who proceedeth from the Father, he shall testify concerning me:
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 And ye also shall bear witness, because ye have been with me from the beginning.
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.

< John 15 >