< Genesis 36 >

1 Now these are the generations of Esau, who is Edom.
Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
2 Esau took his wives of the daughters of Canaan; Adah the daughter of Elon the Hittite, and Aholibamah the daughter of Anah the daughter of Zibeon the Hivite;
Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
3 And Bashemath Ishmael’s daughter, sister of Nebajoth.
ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
4 And Adah bore to Esau Eliphaz; and Bashemath bore Reuel;
Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
5 And Aholibamah bore Jeush, and Jaalam, and Korah: these are the sons of Esau, who were born to him in the land of Canaan.
Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
6 And Esau took his wives, and his sons, and his daughters, and all the persons of his house, and his cattle, and all his beasts, and all his substance, which he had gained in the land of Canaan; and went into the country from the face of his brother Jacob.
Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
7 For their riches were more than that they might dwell together; and the land where they were strangers could not sustain them because of their cattle.
Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
8 Thus dwelt Esau in mount Seir: Esau is Edom.
Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
9 And these are the generations of Esau the father of the Edomites in mount Seir:
Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
10 These are the names of Esau’s sons; Eliphaz the son of Adah the wife of Esau, Reuel the son of Bashemath the wife of Esau.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
11 And the sons of Eliphaz were Teman, Omar, Zepho, and Gatam, and Kenaz.
’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
12 And Timna was concubine to Eliphaz Esau’s son; and she bore to Eliphaz Amalek: these were the sons of Adah Esau’s wife.
Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
13 And these are the sons of Reuel; Nahath, and Zerah, Shammah, and Mizzah: these were the sons of Bashemath Esau’s wife.
’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
14 And these were the sons of Aholibamah, the daughter of Anah the daughter of Zibeon, Esau’s wife: and she bore to Esau Jeush, and Jaalam, and Korah.
’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
15 These were chiefs of the sons of Esau: the sons of Eliphaz the firstborn son of Esau; chief Teman, chief Omar, chief Zepho, chief Kenaz,
Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
16 Chief Korah, chief Gatam, and chief Amalek: these are the chiefs that came of Eliphaz in the land of Edom; these were the sons of Adah.
Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
17 And these are the sons of Reuel Esau’s son; chief Nahath, chief Zerah, chief Shammah, chief Mizzah: these are the chiefs that came of Reuel in the land of Edom; these are the sons of Bashemath Esau’s wife.
’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
18 And these are the sons of Aholibamah Esau’s wife; chief Jeush, chief Jaalam, chief Korah: these were the chiefs that came of Aholibamah the daughter of Anah, Esau’s wife.
’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
19 These are the sons of Esau, who is Edom, and these are their chiefs.
Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
20 These are the sons of Seir the Horite, who inhabited the land; Lotan, and Shobal, and Zibeon, and Anah,
Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
21 And Dishon, and Ezer, and Dishan: these are the chiefs of the Horites, the children of Seir in the land of Edom.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
22 And the children of Lotan were Hori and Hemam; and Lotan’s sister was Timna.
’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
23 And the children of Shobal were these; Alvan, and Manahath, and Ebal, Shepho, and Onam.
’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
24 And these are the children of Zibeon; both Ajah, and Anah: this was that Anah that found the mules in the wilderness, as he fed the donkeys of Zibeon his father.
’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
25 And the children of Anah were these; Dishon, and Aholibamah the daughter of Anah.
’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
26 And these are the children of Dishon; Hemdan, and Eshban, and Ithran, and Cheran.
’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
27 The children of Ezer are these; Bilhan, and Zaavan, and Akan.
’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
28 The children of Dishan are these; Uz, and Aran.
’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
29 These are the chiefs that came of the Horites; chief Lotan, chief Shobal, chief Zibeon, chief Anah,
Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
30 Chief Dishon, chief Ezer, chief Dishan: these are the chiefs that came of Hori, among their chiefs in the land of Seir.
Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
31 And these are the kings that reigned in the land of Edom, before there reigned any king over the children of Israel.
Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
32 And Bela the son of Beor reigned in Edom: and the name of his city was Dinhabah.
Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
33 And Bela died, and Jobab the son of Zerah of Bozrah reigned in his stead.
Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
34 And Jobab died, and Husham of the land of Temani reigned in his stead.
Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
35 And Husham died, and Hadad the son of Bedad, who smote Midian in the field of Moab, reigned in his stead: and the name of his city was Avith.
Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
36 And Hadad died, and Samlah of Masrekah reigned in his stead.
Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
37 And Samlah died, and Saul of Rehoboth by the river reigned in his stead.
Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
38 And Saul died, and Baalhanan the son of Achbor reigned in his stead.
Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
39 And Baalhanan the son of Achbor died, and Hadar reigned in his stead: and the name of his city was Pau; and his wife’s name was Mehetabel, the daughter of Matred, the daughter of Mezahab.
Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
40 And these are the names of the chiefs that came of Esau, according to their families, after their places, by their names; chief Timnah, chief Alvah, chief Jetheth,
Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
41 Chief Aholibamah, chief Elah, chief Pinon,
Oholibama, Ela, Finon.
42 Chief Kenaz, chief Teman, chief Mibzar,
Kenaz, Teman, Mibzar.
43 Chief Magdiel, chief Iram: these are the chiefs of Edom, according to their habitations in the land of their possession: he is Esau the father of the Edomites.
Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.

< Genesis 36 >