< Exodus 13 >

1 And the LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Sanctify to me all the firstborn, whatever openeth the womb among the children of Israel, both of man and of beast: it is mine.
“Keɓe mini kowane ɗan fari. Ɗan fari wanda ya fara buɗe mahaifa a cikin Isra’ilawa nawa ne, ko na mutum ko na dabba.”
3 And Moses said to the people, Remember this day, when ye came out from Egypt, out of the house of bondage; for by strength of hand the LORD brought you out from this place: there shall no leavened bread be eaten.
Sai Musa ya ce wa mutane, “Ku tuna da wannan rana, ranar da kuka fito daga Masar, daga ƙasar bauta, gama Ubangiji ya fito da ku da hannu mai iko. Kada ku ci wani abin da yake da yisti.
4 This day in the month Abib, ye came out.
A wannan rana kuka fita, wato, a watan Abib.
5 And it shall be when the LORD shall bring thee into the land of the Canaanites, and the Hittites, and the Amorites, and the Hivites, and the Jebusites, which he swore to thy fathers to give thee, a land flowing with milk and honey, that thou shalt keep this service in this month.
Sa’ad da Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku, ƙasar da take zub da madara da zuma, za ku kiyaye wannan biki a wannan wata.
6 Seven days shalt thou eat unleavened bread, and in the seventh day shall be a feast to the LORD.
Kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, a kan rana ta bakwai kuma za ku yi biki ga Ubangiji.
7 Unleavened bread shall be eaten seven days; and there shall no leavened bread be seen with thee, neither shall there be leaven seen with thee in all thy quarters.
Ku ci burodi marar yisti cikin kwana bakwai; kada a sami wani abu mai yisti a cikinku, ko a sami yisti a ko’ina a wurinku.
8 And thou shalt show thy son in that day, saying, This is done because of that which the LORD did to me when I came forth out of Egypt.
A ranan nan kowa zai faɗa wa ɗanka, ‘Ina yin haka saboda abin da Ubangiji ya yi mini, sa’ad da na fita daga Masar.’
9 And it shall be for a sign to thee upon thy hand, and for a memorial between thy eyes, that the LORD’S law may be in thy mouth: for with a strong hand hath the LORD brought thee out of Egypt.
Wannan abin tunawa zai zama muku alama a hannunku, da kuma a goshinku cewa dokar Ubangiji tana a bakinku. Gama Ubangiji ya fitar da ku daga Masar da hannu mai iko.
10 Thou shalt therefore keep this ordinance in its season from year to year.
Dole ku kiyaye wannan farilla kowace shekara a lokacinta.
11 And it shall be when the LORD shall bring thee into the land of the Canaanites, as he swore to thee and to thy fathers, and shall give it to thee,
“Bayan Ubangiji ya kawo ku cikin ƙasar Kan’aniyawa, ya kuma ba da ita yadda ya alkawarta muku da rantsuwa, ku da kakanninku,
12 That thou shall set apart to the LORD all that openeth the womb, and every firstling that cometh of a beast which thou hast; the males shall be the LORD’S.
sai ku miƙa kowane ɗan fari ga Ubangiji. Duk ɗan farin dabbobinku na Ubangiji ne.
13 And every firstling of a donkey thou shalt redeem with a lamb; and if thou wilt not redeem it, then thou shalt break his neck: and all the firstborn of man among thy children shalt thou redeem.
Amma a fanshi kowane ɗan farin jakinku da ɗan rago. In kuwa ba za ku fanshe shi ba, sai ku karye wuyansa. Sai ku fanshe kowane ɗan farin daga cikin’ya’yanku.
14 And it shall be when thy son asketh thee in time to come, saying, What is this? that thou shalt say to him, By strength of hand the LORD brought us out from Egypt, from the house of bondage:
“A kwanaki masu zuwa, in ɗanka ya tambaye ka, ‘Mene ne manufar wannan?’ Ka faɗa masa cewa, ‘Da hannu mai iko Ubangiji ya fito da mu daga Masar, daga ƙasar bauta.
15 And it came to pass, when Pharaoh would hardly let us go, that the LORD slew all the firstborn in the land of Egypt, both the firstborn of man, and the firstborn of beasts: therefore I sacrifice to the LORD all that openeth the womb, being males; but all the firstborn of my children I redeem.
Sa’ad da Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai yarda ya sallame mu ba, sai Ubangiji ya kashe dukan’ya’yan farin ƙasar Masar, na mutum da na dabba, gaba ɗaya. Domin haka nake yin hadaya ga Ubangiji da’ya’yan fari, maza, da suka fara buɗe mahaifa, amma nakan fanshi dukan’ya’yan farina maza.’
16 And it shall be for a token upon thy hand, and for frontlets between thy eyes: for by strength of hand the LORD brought us forth out of Egypt.
Za tă kuma zama alama a hannunku da kuma shaida a goshinku cewa Ubangiji ya fito da mu daga Masar da hannunsa mai iko.”
17 And it came to pass, when Pharaoh had let the people go, that God led them not through the way of the land of the Philistines, although that was near; for God said, Lest the people repent when they see war, and they return to Egypt:
Sa’ad da Fir’auna ya bar mutane su tafi, Allah bai bi da su a hanyar da ta bi ta iyakar Filistiyawa ba, ko da yake wannan hanya ce ta fi kusa. Gama Allah ya ce, “In suka fuskanci yaƙi, wataƙila su canja ra’ayinsu su koma Masar.”
18 But God led the people about, through the way of the wilderness of the Red sea: and the children of Israel went up armed from the land of Egypt.
Saboda haka Allah ya kewaye da mutanen ta hamada zuwa Jan Teku. Isra’ilawa kuwa suka fita daga Masar da shirin yaƙi.
19 And Moses took the bones of Joseph with him: for he had solemnly sworn the children of Israel, saying, God will surely visit you; and ye shall carry up my bones from here with you.
Musa ya ɗauki ƙasusuwan Yusuf tare da shi, gama Yusuf ya sa Isra’ilawa su rantse masa. Ya ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, sai ku ɗibi ƙasusuwana tare da ku daga wannan wuri.”
20 And they took their journey from Succoth, and encamped in Etham, in the edge of the wilderness.
Bayan sun bar Sukkot sai suka kafa sansani a Etam a bakin hamada.
21 And the LORD went before them by day in a pillar of a cloud, to lead them in the way; and by night in a pillar of fire, to give them light; to go by day and night:
Da rana Ubangiji yakan ja gabansu a cikin al’amudin girgije domin yă bishe su a kan hanyarsu, da dare kuma a cikin al’amudin wuta domin yă ba su haske, domin su iya tafiya dare da rana.
22 He took not away the pillar of the cloud by day, nor the pillar of fire by night, from before the people.
Al’amudan nan biyu, na girgije da na wuta, ba su daina yi wa jama’a jagora ba.

< Exodus 13 >