< 1 Chronicles 14 >

1 Now Hiram king of Tyre sent messengers to David, and timber of cedars, with masons and carpenters, to build him an house.
To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
2 And David perceived that the LORD had confirmed him king over Israel, for his kingdom was exalted on high, because of his people Israel.
Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
3 And David took more wives at Jerusalem: and David begat more sons and daughters.
A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
4 Now these are the names of his children which he had in Jerusalem; Shammua, and Shobab, Nathan, and Solomon,
Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
5 And Ibhar, and Elishua, and Elpalet,
Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
6 And Nogah, and Nepheg, and Japhia,
Noga, Nefeg, Yafiya,
7 And Elishama, and Beeliada, and Eliphalet.
Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
8 And when the Philistines heard that David was anointed king over all Israel, all the Philistines went up to seek David. And David heard of it, and went out against them.
Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
9 And the Philistines came and spread themselves in the valley of Rephaim.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
10 And David enquired of God, saying, Shall I go up against the Philistines? and wilt thou deliver them into my hand? And the LORD said to him, Go up; for I will deliver them into thy hand.
sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
11 So they came up to Baalperazim; and David smote them there. Then David said, God hath broken in upon my enemies by my hand like the breaking forth of waters: therefore they called the name of that place Baalperazim.
Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
12 And when they had left their gods there, David gave a commandment, and they were burned with fire.
Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
13 And the Philistines yet again spread themselves abroad in the valley.
Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
14 Therefore David enquired again of God; and God said to him, Go not up after them; turn away from them, and come upon them in front of the mulberry trees.
sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
15 And it shall be, when thou shalt hear a sound of marching in the tops of the mulberry trees, then thou shalt go out to battle: for God hath gone forth before thee to smite the host of the Philistines.
Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
16 David therefore did as God commanded him: and they smote the host of the Philistines from Gibeon even to Gazer.
Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
17 And the fame of David went out into all lands; and the LORD brought the fear of him upon all nations.
Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.

< 1 Chronicles 14 >