< Luke 1 >

1 Many have taken on the work of putting together an account of the things that have been fulfilled among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 just as they were passed down to us by those who from the first were eyewitnesses and servants of the word.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 So it seemed good to me also, because I have accurately investigated everything from the beginning, to write an orderly account for you, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 so that you might know the certainty of the things you have been taught.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 In the days of Herod, king of Judea, there was a certain priest named Zechariah, from the division of Abijah. His wife was from the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were both righteous before God, obeying all the commandments and ordinances of the Lord.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no child, because Elizabeth was barren, and they were both very old by this time.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Now it came about that Zechariah was in God's presence, carrying out the priestly duties in the order of his division.
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 According to the customary way of choosing which priest would serve, he had been chosen by lot to enter into the temple of the Lord to burn incense.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 The whole crowd of people was praying outside at the hour when the incense was burned.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Now an angel of the Lord appeared to him and stood at the right side of the incense altar.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 When Zechariah saw him, he was terrified and fear fell on him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah, because your prayer has been heard. Your wife Elizabeth will bear you a son. You will call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 You will have joy and gladness, and many will rejoice at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the sight of the Lord. He must never drink wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit from his mother's womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Many of the people of Israel will be turned to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 He will go before the face of the Lord in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of the fathers to the children and the disobedient to the wisdom of the righteous—to make ready for the Lord a people prepared for him.”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zechariah said to the angel, “How can I know this? For I am an old man and my wife is very old.”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 The angel answered and said to him, “I am Gabriel, who stands in the presence of God. I was sent to speak to you, to bring you this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Behold! You will be silent, unable to speak, until the day these things take place. This is because you did not believe my words, which will be fulfilled at the right time.”
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Now the people were waiting for Zechariah. They were surprised that he was spending so much time in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 But when he came out, he could not speak to them. They realized that he had seen a vision while he was in the temple. He kept on making signs to them and remained silent.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 It came about that when the days of his service were over, he went to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 After these days, his wife Elizabeth conceived and for five months she kept herself hidden. She said,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 “This is what the Lord has done for me when he looked at me with favor in order to take away my shame before people.”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 In the sixth month, the angel Gabriel was sent from God to a city in Galilee named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin engaged to a man whose name was Joseph. He belonged to the house of David, and the virgin's name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 He came to her and said, “Greetings, you who are highly favored! The Lord is with you.”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But she was very confused by his words and she wondered what kind of greeting this could be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 The angel said to her, “Do not be afraid, Mary, for you have found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 See, you will conceive in your womb and bear a son. You will call his name 'Jesus.'
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great and will be called the Son of the Most High. The Lord God will give him the throne of his ancestor David.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 He will reign over the house of Jacob forever, and there will be no end to his kingdom.” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Mary said to the angel, “How will this happen, since I have not slept with any man?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 The angel answered and said to her, “The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will come over you. So the holy one to be born will be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 See, your relative Elizabeth has also conceived a son in her old age. This is the sixth month for her, she who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For nothing will be impossible for God.”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Mary said, “See, I am the female servant of the Lord. Let it be for me according to your message.” Then the angel left her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Then Mary arose in those days and quickly went into the hill country, to a city in Judea.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 She went into the house of Zechariah and greeted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Now it happened that when Elizabeth heard Mary's greeting, the baby in her womb jumped, and Elizabeth was filled with the Holy Spirit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 She raised her voice and said loudly, “Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Why has it happened to me that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For see, when the sound of your greeting came to my ears, the baby in my womb jumped for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Blessed is she who believed that there would be a fulfillment of the things that were told her from the Lord.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Mary said, “My soul praises the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit has rejoiced in God my savior.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 For he has looked at the low condition of his female servant. For see, from now on all generations will call me blessed.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For he who is mighty has done great things for me, and his name is holy.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 His mercy lasts from generation to generation for those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He has displayed strength with his arm; he has scattered those who were proud about the thoughts of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has thrown down princes from their thrones and he has raised up those of low condition.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He has filled the hungry with good things, but the rich he has sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He has given help to Israel his servant, so as to remember to show mercy
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (as he said to our fathers) to Abraham and his descendants forever.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Mary stayed with Elizabeth about three months and then returned to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now the time had come for Elizabeth to deliver her baby and she gave birth to a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Her neighbors and her relatives heard that the Lord had shown his great mercy to her, and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Now it happened on the eighth day that they came to circumcise the child. They would have called him “Zechariah,” after the name of his father.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 But his mother answered and said, “No. He will be called John.”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 They said to her, “There is no one among your relatives who is called by this name.”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 They made signs to his father as to how he wanted him to be named.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 His father asked for a writing tablet and wrote, “His name is John.” They all were astonished at this.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Immediately his mouth was opened and his tongue was freed. He spoke and praised God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Fear came on all who lived around them. All these matters were spread throughout all the hill country of Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 All who heard them stored them in their hearts, saying, “What then will this child become?” For the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 His father Zechariah was filled with the Holy Spirit and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Praised be the Lord, the God of Israel, for he has come to help and he has accomplished redemption for his people.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 He has raised up a horn of salvation for us in the house of his servant David
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (as he spoke by the mouth of his holy prophets from long ago), (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies and from the hand of all who hate us.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 He will do this to show mercy to our fathers and to remember his holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath that he spoke to Abraham our father.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 He swore to grant to us that we, having been delivered out of the hand of our enemies, would serve him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in holiness and righteousness before him all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Yes, and you, child, will be called a prophet of the Most High, for you will go before the face of the Lord to prepare his paths, to prepare people for his coming,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give knowledge of salvation to his people by the forgiveness of their sins.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 This will happen because of the tender mercy of our God, because of which the sunrise from on high will come to help us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to shine on those who sit in darkness and in the shadow of death. He will do this to guide our feet into the path of peace.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Now the child grew and became strong in spirit, and he was in the wilderness until the day of his public appearance to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >