< Genesis 19 >

1 The two angels came to Sodom in the evening, while Lot was sitting at the gate of Sodom. Lot saw them, arose to meet them, and bowed down with his face to the ground.
Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
2 He said, “Please my masters, I urge you to turn aside into your servant's house, stay for the night, and wash your feet. Then you can rise up early and go on your way.” They replied, “No, we will spend the night in the town square.”
Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
3 But he urged them strongly, so they went with him, and entered into his house. He prepared a meal and baked unleavened bread, and they ate.
Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
4 But before they lay down, the men of the city, the men of Sodom, surrounded the house, both young and old, all the men from every part of the city.
Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
5 They called to Lot, and said to him, “Where are the men that came in to you tonight? Bring them out to us, that we may sleep with them.”
Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
6 So Lot went out the door to them and shut the door after himself.
Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
7 He said, “I beg you, my brothers, do not act so wickedly.
ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
8 Look, I have two daughters who have not slept with any man. Let me, I beg you, bring them out to you, and you do to them whatever is good in your eyes. Only do nothing to these men, because they have come under the shadow of my roof.”
Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
9 They said, “Stand back!” They also said, “This one came here to live as a foreigner, and now he has become our judge! Now we will deal worse with you than with them.” They pressed hard against the man, against Lot, and came near to break down the door.
Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
10 But the men reached out their hands and brought Lot into the house with them and shut the door.
Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
11 Then Lot's visitors struck with blindness the men who were outside the door of the house, both young and old, so that they became exhausted when they were trying to find the door.
Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
12 Then the men said to Lot, “Do you have anyone else here? Any sons-in-law, your sons and your daughters, and whoever you have in the city, get them out of here.
Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
13 For we are about to destroy this place, because the accusations against it before Yahweh have become so loud that he has sent us to destroy it.”
gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
14 Lot went out and spoke to his sons-in-law, the men who had promised to marry his daughters, and said, “Quick, get out of this place, for Yahweh is about to destroy the city.” But to his sons-in-law he seemed to be joking.
Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
15 When the morning dawned, the angels urged Lot, saying, “Get going, take your wife and your two daughters that are here, so you are not swept away in the punishment of the city.”
Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
16 But he lingered. So the men grabbed his hand, and the hand of his wife, and the hands of his two daughters, because Yahweh was merciful to him. They brought them out, and set them outside the city.
Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
17 When they had brought them out, one of the men said, “Run for your lives! Do not look back, or stay anywhere on the plain. Escape to the mountains so you are not swept away.”
Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
18 Lot said to them, “No, please, my masters!
Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
19 Your servant has found favor in your eyes, and you have shown me great kindness in saving my life, but I cannot escape to the mountains, because the disaster will overtake me, and I will die.
Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
20 Look, that city over there is near enough to flee to, and it is a little one. Please, let me escape there (is it not a little one?), and my life will be saved.”
Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
21 He said to him, “Alright, I am granting this request also, that I will not destroy the city which you have mentioned.
Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
22 Hurry! Escape there, for I cannot do anything until you arrive there.” Therefore the city was called Zoar.
Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
23 The sun had risen upon the earth when Lot reached Zoar.
A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
24 Then Yahweh rained down upon Sodom and Gomorrah sulfur and fire from Yahweh out of the sky.
Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
25 He destroyed those cities, and all the plain, and all the inhabitants of the cities, and the plants that grew on the ground.
Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
26 But Lot's wife, who was behind him, looked back, and she became a pillar of salt.
Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
27 Abraham got up early in the morning and went to the place where he had stood before Yahweh.
Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
28 He looked down toward Sodom and Gomorrah and toward all the land of the plain. He looked and behold, smoke was rising from the land like the smoke of a furnace.
Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
29 So when God destroyed the cities of the plain, God called Abraham to mind. He sent Lot out of the midst of the destruction when he destroyed the cities in which Lot had lived.
Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
30 But Lot went up from Zoar to live in the mountains with his two daughters, because he was afraid to live in Zoar. So he lived in a cave, he and his two daughters.
Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
31 The firstborn said to the younger, “Our father is old, and there is no man anywhere to sleep with us according to the way of all the world.
Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
32 Come, let us make our father drink wine, and we will sleep with him, so that we may extend our father's line.”
Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
33 So they made their father drink wine that night. Then the firstborn went in and slept with her father; he did not know when she lay down, nor when she arose.
A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
34 The next day the firstborn said to the younger, “Listen, last night I slept with my father. Let us make him drink wine tonight also, and you should go in and sleep with him, so that we may extend our father's line.”
Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
35 So they made their father drink wine that night also, and the younger went and slept with him. He did not know when she lay down, nor when she arose.
Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
36 So both the daughters of Lot were pregnant by their father.
Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
37 The firstborn gave birth to a son, and named him Moab. He became the ancestor of the Moabites of today.
’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
38 As for the younger daughter, she also gave birth to a son, and named him Ben-Ammi. He became the ancestor of the people of Ammon of today.
’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.

< Genesis 19 >