< 2 Kings 13 >

1 In the twenty-third year of Joash son of Ahaziah king of Judah, Jehoahaz son of Jehu began to reign over Israel in Samaria; he reigned seventeen years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 He did what was evil in the sight of Yahweh and followed the sins of Jeroboam son of Nebat, who caused Israel to sin; and Jehoahaz did not turn away from them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 The anger of Yahweh burned against Israel, and he gave them continually into the hand of Hazael king of Aram and into the hand of Ben Hadad son of Hazael.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 So Jehoahaz implored Yahweh, and Yahweh listened to him because he saw the oppression of Israel, how the king of Aram was oppressing them.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 So Yahweh gave Israel a rescuer, and they escaped from the hand of the Arameans, and the people of Israel began to live in their homes as they had before.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Nevertheless, they did not depart from the sins of the house of Jeroboam, who caused Israel to sin, and they continued in them; and the Asherah pole remained in Samaria.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 The Arameans left Jehoahaz with only fifty horsemen, ten chariots, and ten thousand footmen, for the king of Aram had destroyed them and made them like the chaff at threshing time.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 As for the other matters concerning Jehoahaz, and all that he did and his power, are they not written in the book of the events of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 So Jehoahaz slept with his ancestors, and they buried him in Samaria. Johoash his son became king in his place.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 In the thirty-seventh year of Joash king of Judah, the reign of Jehoash son of Jehoahaz began over Israel in Samaria; he reigned sixteen years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 He did what was evil in the sight of Yahweh. He did not leave behind any of the sins of Jeroboam son of Nebat, by which he had made Israel to sin, but he walked in them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 As for the other matters concerning Jehoash, and all that he did, and his might by which he fought against Amaziah king of Judah, are they not written in the book of the events of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 Jehoash slept with his ancestors, and Jeroboam sat on his throne. Jehoash was buried in Samaria with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Now Elisha became sick with an illness by which he later died, so Jehoash the king of Israel came down to him and wept over him. He said, “My father, my father, the chariots of Israel and the horsemen are taking you away!”
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Elisha said to him, “Pick up a bow and some arrows,” so Joash picked up a bow and some arrows.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Elisha said to the king of Israel, “Put your hand on the bow,” so he put his hand on it. Then Elisha laid his hands on the king's hands.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 Elisha said, “Open the window eastward,” so he opened it. Then Elisha said, “Shoot!”, and he shot. Elisha said, “This is Yahweh's arrow of victory, the arrow of victory over Aram, for you will attack the Arameans in Aphek until you have consumed them.”
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Then Elisha said, “Take the arrows,” so Joash took them. He said to the king of Israel, “Strike the ground with them,” and he struck the ground three times, then stopped.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 But the man of God was angry with him and said, “You should have hit the ground five or six times. Then you would have attacked Aram until you annihilated it, but now you will attack Aram only three times.”
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Then Elisha died, and they buried him. Now groups of Moabites invaded the land at the beginning of the year.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 As they were burying a certain man, they saw a group of Moabites, so they threw the body into Elisha's grave. As soon as the man touched Elisha's bones, he revived and stood up on his feet.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Hazael king of Aram oppressed Israel all the days of Jehoahaz.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 But Yahweh was gracious to Israel, and had compassion on them and concern for them, because of his covenant with Abraham, Isaac, and Jacob. So Yahweh did not destroy them, and he still has not driven them away from his presence.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 Hazael king of Aram died, and Ben Hadad his son became king in his place.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Jehoash son of Jehoahaz took back from Ben Hadad son of Hazael the cities that had been taken from Jehoahaz his father by war. Jehoash attacked him three times, and he recovered those cities of Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >