< Luke 18 >

1 And he put forth a similitude vnto the signifyinge that men ought alwayes to praye and not to be wery
Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
2 sayinge: Ther was a Iudge in a certayne cite which feared not god nether regarded man.
Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
3 And ther was a certayne wedowe in the same cite which came vnto him sayinge: avenge me of myne adversary.
A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
4 And he wolde not for a whyle. But afterwarde he sayd vnto him selfe: though I feare not God nor care for man
“An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
5 yet because this wedowe troubleth me I will avenge her lest at the laste she come and hagge on me.
amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
6 And the lorde sayd: heare what the vnrightewes Iudge sayeth.
Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
7 And shall not god avenge his electe which crye daye and nyght vnto him ye though he differre them?
Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
8 I tell you he will avenge them and that quickly. Neverthelesse when the sonne of man cometh suppose ye that he shall fynde faithe on the erthe.
Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
9 And he put forthe this similitude vnto certayne which trusted in the selves yt they were perfecte and despysed other.
Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
10 Two men went vp into ye teple to praye: ye one a pharise and the other a publican.
“Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
11 The pharise stode and prayed thus wt him selfe. God I thanke the yt I am not as other men are extorsioners vniuste advoutrers or as this publican.
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
12 I fast twyse in ye weke. I geve tythe of all that I possesse.
Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
13 And the publican stode afarre of and wolde not lyfte vp his eyes to heven but smote his brest sayinge: God be mercyfull to me a synner.
“Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
14 I tell you: this ma departed hoe to his housse iustified moore then the other. For every man that exalteth him selfe shalbe brought low: And he yt hubleth him selfe shalbe exalted
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
15 They brought vnto him also babes yt he shuld touche the. When his disciples sawe that they rebuked the.
Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
16 But Iesus called the vnto him and sayde: Suffre chyldren to come vnto me and forbidde the not. For of soche is ye kyngdome of God.
Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
17 Verely I saye vnto you: whosoever receaveth not the kyngdome of God as a chylde: he shall not enter therin.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
18 And a certayne ruler axed him sayinge: Good Master: what ought I to do to obtayne eternall lyfe? (aiōnios g166)
Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
19 Iesus sayd vnto him: Why callest thou me good? No man is good save God only.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
20 Thou knowest ye comaundmentes: Thou shalt not commit advoutry: thou shalt not kyll: thou shalt not steale: thou shalt not beare false witnes: Honoure thy father and thy mother.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
21 And he sayde: all these have I kept from my youthe.
Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
22 When Iesus hearde that he sayde vnto him: Yet lackest thou one thinge. Sell all that thou hast and distribute it vnto the poore and thou shalt have treasure in heven and come and folowe me.
Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
23 When he heard that he was hevy: for he was very ryche.
Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
24 When Iesus sawe him morne he sayde: with what difficulte shall they that have ryches enter into the kyngdome of God:
Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
25 it is easyer for a camell to goo thorow a nedles eye then for a ryche man to enter into the kyngdome of God.
Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
26 Then sayde they that hearde that: And who shall then be saved?
Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
27 And he sayde: Thinges which are vnpossible with men are possible with God.
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
28 Then Peter sayde: Loo we have lefte all and have folowed the.
Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
29 And he sayde vnto them: Verely I saye vnto you ther is noo man that leaveth housse other father and mother other brethren or wyfe or chyldren for the kyngdome of Goddes sake
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
30 which same shall not receave moche moore in this worlde: and in the worlde to come lyfe everlastinge. (aiōn g165, aiōnios g166)
da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
31 He toke vnto him twelve and sayde vnto them. Beholde we go vp to Ierusalem and all shalbe fulfilled that are written by ye Prophetes of the sonne of man.
Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
32 He shalbe delivered vnto the gentils and shalbe mocked and shalbe despytfully entreated and shalbe spetted on:
Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
33 and when they have scourged him they will put him to deeth and the thyrde daye he shall aryse agayne.
za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
34 But they vnderstode none of these thinges. And this sayinge was hid fro them. And they perceaved not the thinges which were spoken.
Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
35 And it came to passe as he was come nye vnto Hierico a certayne blynde man sate by the waye syde begginge.
Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
36 And when he hearde the people passe by he axed what it meant.
Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
37 And they sayde vnto him yt Iesus of Nazareth passed by.
Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
38 And he cryed sayinge: Iesus ye sonne of David have thou mercy on me.
Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
39 And they which went before rebuked him that he shuld holde his peace. But he cryed so moche the moare thou sonne of David have mercy on me.
Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
40 And Iesus stode styll and commaunded him to be brought vnto him. And when he was come neare he axed him
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
41 sayinge: What wilt thou that I do vnto the? And he sayde: Lorde yt I maye receave my sight.
“Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
42 Iesus sayde vnto him: receave thy sight: thy faith hath saved the.
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
43 And immediatly he sawe and folowed him praysinge God. And all the people when they sawe it gave laude to God.
Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.

< Luke 18 >