< Acts 26 >

1 Agrippa sayde vnto Paul: thou arte permitted to speake for thy selfe. Then Paul stretched forth the honde and answered for him selfe.
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
2 I thynke my selfe happy kynge Agrippa because I shall answere this daye before the of all the thinges wherof I am accused of ye Iewes
Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
3 namely because thou arte experte in all customes and questions which are amonge the Iewes. Wherfore I beseche the to heare me paciently.
musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
4 My lyvynge of a chylde which was at the fyrst amoge myne awne nacion at Ierusalem knowe all the Iewes
“Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
5 which knew me from ye beginnynge yf they wolde testifie it. For after the most straytest secte of oure laye lyved I a pharisaye.
Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
6 And now I stond and am iudged for the hope of the promes made of God vnto oure fathers:
Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
7 vnto which promes oure. xii. tribes instantly servynge God daye and nyght hope to come. For which hopes sake kynge Agrippa am I accused of the Iewes.
Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
8 Why shuld it be thought a thinge vncredible vnto you that god shuld rayse agayne the deed?
Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
9 I also verely thought in my selfe that I ought to do many cotrary thinges clene agaynst the name of Iesus of Nazareth:
“Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
10 which thinge I also dyd in Ierusalem. Where many of the sainctes I shut vp in preson and had receaved auctorite of ye hye prestes. And whe they were put to deeth I gave the sentence.
Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
11 And I punysshed them ofte in every synagoge and compelled them to blaspheme: and was yet more mad apon them and persecuted the even vnto straunge cities.
Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
12 About the which thinges as I went to Damasco with auctorite and licence of the hye Prestes
“A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
13 even at myddaye (o kynge) I sawe in ye waye a lyght from heven above the brightnes of the sunne shyne rounde about me and them which iorneyed with me.
Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
14 When we were all fallen to the erth I hearde a voyce speakynge vnto me and sayinge in ye Hebrue tonge: Saul Saul why persecutest thou me? It is harde for the to kicke agaynste the pricke.
Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
15 And I sayde: Who arte thou lorde? And he sayde I am Iesus whom thou persecutest.
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
16 But ryse and stond vp on thy fete. For I have apered vnto the for this purpose to make the a minister and a witnes both of tho thinges which thou hast sene and of tho thinges in the which I will appere vnto the
Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
17 delyverynge the from the people and from ye gentyls vnto which nowe I sende the
Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
18 to open their eyes that they myght turne from darcknes vnto lyght and from the power of Satan vnto God that they maye receave forgevenes of synnes and inheritauce amonge the which are sanctified by fayth in me.
ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
19 Wherfore kynge Agrippa I was not disobedient vnto the hevenly vision:
“Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
20 but shewed fyrst vnto them of Damasco and at Ierusalem and thorow out all the costes of Iewry and to the gentyls that they shuld repent and turne to God and do the ryght workes of repentaunce.
Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
21 For this cause the Iewes caught me in the temple and went about to kyll me.
Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
22 Neverthelesse I obtayned helpe of God and cotynew vnto this daye witnessyng bothe to small and to greate saying none other thinges then those which the prophetes and Moses dyd saye shuld come
Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
23 that Christ shulde suffre and that he shuld be the fyrst that shulde ryse from deeth and shuld shewe lyght vnto the people and the gentyls.
cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
24 As he thus answered for him selfe: Festus sayde with a lowde voyce: Paul thou arte besides thy selfe. Moche learnynge hath made the mad.
A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
25 And Paul sayde: I am not mad most dere Festus: but speake the wordes of trueth and sobernes.
Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
26 The kynge knoweth of these thinges before whom I speke frely: nether thynke I that eny of these thinges are hydden fro him. For this thinge was not done in a corner.
Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
27 Kynge Agrippa belevest thou ye prophetes? I wote well thou belevest.
Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
28 Agrippa sayde vnto Paul: Sumwhat thou bringest me in mynde for to be come a Christen.
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
29 And Paul sayd: I wolde to God that not only thou: but also all that heare me to daye were not sumwhat only but altogeder soche as I am except these bondes.
Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
30 And when he had thus spoken the kynge rose vp and the debite and Bernice and they that sate with them.
Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
31 And when they were gone aparte they talked betwene them selves sayinge: This man doeth nothinge worthy of deeth nor of bondes.
Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
32 Then sayde Agrippa vnto Festus: This man myght have bene lowsed yf he had not appealed vnto Cesar.
Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”

< Acts 26 >