< Revelation 19 >

1 After this, I heard what seemed to be a great shout from a vast throng in Heaven, crying — ‘Hallelujah! To our God belong Salvation, and Glory, and Power,
Bayan wadannan abubuwa na ji wata karar da ta yi kamar muryar mutane masu yawa a sama suna cewa, “Halleluya. Ceto, daukaka da iko sun tabbata ga Allahnmu.
2 for true and righteous are his judgments. For he has passed judgment upon the Great Harlot who was corrupting the earth by her licentiousness, and he has taken vengeance upon her for the blood of his servants.’
Hukunce - hukuncensa gaskiya ne da adalci, domin ya hukunta babbar karuwan nan wadda ta kazamtar da duniya da fasikancinta. Ya dauki fansar jinin bayinsa, wadda ita da kanta ta zubar.”
3 Again they cried — ‘Hallelujah!’ And the smoke from her ruins rises for ever and ever. (aiōn g165)
Suka yi magana a karo na biyu: “Halleluya! Hayaki na tasowa daga wurinta har abada abadin.” (aiōn g165)
4 Then the twenty-four Councillors and the Four Creatures prostrated themselves and worshiped God who was seated upon the throne, crying — ‘Amen, Hallelujah!’;
Dattawan nan ashirin da hudu da rayayyun halittun nan hudu, suka fadi suka yi wa Allah sujada shi da yake zaune a kan kursiyin. Suna cewa, “Amin. Halleluya!”
5 and from the throne there came a voice which said — ‘Praise our God all you who serve him, You who reverence him, both high and low.’
Sai wata murya ta fito daga kursiyin tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, dukanku bayinsa, ku da kuke tsoronsa, da duk marasa iko da masu iko.”
6 Then I heard ‘what seemed to be the shout of a vast throng, like the sound of many waters,’ and like the sound of loud peals of thunder, crying — ‘Hallelujah! For the Lord is King, our God, the Almighty.
Sai na ji murya kamar na kasaitaccen taron mutane, kamar rurin kogi na ruwaye masu yawa, kuma kamar tsawar aradu, cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji yana mulki, Allah mai iko duka.
7 Let us rejoice and exalt; and we will pay him honour, for the hour for the Marriage of the Lamb has come, and his Bride has made herself ready.
Bari mu yi murna, mu yi farinciki matuka mu kuma ba shi daukaka domin bikin auren Dan Ragon ya zo, amaryarsa kuma ta shirya kanta.
8 And to her it has been granted to robe herself in fine linen, white and pure, for that linen is the good deeds of the People of Christ.’
An yardar mata ta sa kaya masu haske da tsabta na lilin mai laushi” (domin lilin mai laushi shine ayyukan adalci na tsarkaka).
9 Then a voice said to me ‘Write — “Blessed are those who have been summoned to the marriage feast of the Lamb.”’ And the voice said — ‘These words of God are true.’
Mala'ika ya ce mani, “Rubuta wannan: Masu albarka ne wadanda aka gayyace su zuwa bikin auren Dan Ragon.” Ya kuma ce mani, “Wadannan kalmomin Allah na gaskiya ne.”
10 I prostrated myself at the feet of him who spoke to worship him, but he said to me — ‘Forbear; I am your fellow-servant, and the fellow-servant of your Brothers who bear their testimony to Jesus. Worship God. For to bear testimony to Jesus needs the inspiration of the Prophets.’
Na fadi a gaban kafafunsa domin in yi masa sujada, amma ya ce mani, “Kada ka yi haka! Ni ma abokin bauta ne tare da kai da 'yan'uwanka wadanda ke rike da shaida game da Yesu. Yi wa Allah sujada, domin shaida game da Yesu shine ruhun annabci.”
11 Then I saw that Heaven lay open. There appears a white horse; its rider is called ‘Faithful’ and ‘True’; righteously does he judge and make war.
Sai na ga sama a bude, na kuma duba sai ga wani farin doki. Mahayinsa ana kiransa amintacce da gaskiya. Yana shari'a da adalci yana yaki.
12 His eyes are flaming fires; on his head there are many diadems, and he bears a name, written, which no one knows but himself;
Idanunsa kamar harshen wuta suke, a kansa akwai kambuna da yawa. Yana da suna a rubuce a jikinsa wanda ba wani da ya sani sai dai shi da kansa.
13 he has been clothed in a garment sprinkled with blood; and the name by which he is called is ‘The Word of God.’
Yana sanye da riga da aka tsoma a cikin jini, kuma ana kiran sunansa Kalmar Allah.
14 The armies of Heaven followed him, mounted on white horses and clothed in fine linen, white and pure.
Rundunonin sama suna biye da shi a kan fararen dawakai, suna sanye da lilin mai laushi, fari mai tsabta.
15 From his mouth comes a sharp sword, with which ‘to smite the nations; and he will rule them with an iron rod.’ He ‘treads the grapes in the press’ of the maddening wine of the Wrath of Almighty God;
Daga cikin bakinsa takobi mai kaifi na fitowa, da ita yake sarar al'ummai, zai kuma mulke su da sandar karfe. Yana tattake wurin matsar ruwan inabi da matsananciyar fushin Allah Mai iko duka.
16 and on his robe and on his thigh he has this name written — ‘KING OF KINGS AND LORD OF LORDS.’
Yana da suna a rubuce a rigarsa da cinyarsa: “Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji.”
17 Then I saw an angel standing on the sun. He cried in a loud voice to all the birds that fly in mid-heaven — ‘Gather and come to the great feast of God,
Na ga mala'ika tsaye a rana. Yayi kira da murya mai karfi ga dukan tsuntsaye da ke firiya a sama.
18 to eat the flesh of kings, and the flesh of commanders, and the flesh of mighty men, and the flesh of horses and their riders, and the flesh of all freemen and slaves, and of high and low.’
“Ku zo, ku tattaru saboda babban bukin Allah. Ku zo ku ci naman sarakuna, da naman sarakunan yaki, da naman manyan mutane, da naman dawakai, da na mahayansu, da naman dukan mutane, yantattu da bayi, marasa iko da masu iko.”
19 Then I saw the Beast and the kings of the earth and their armies, gathered together to fight with him who sat on the horse and with his army.
Na ga dabban da sarakunan duniya da rundunoninsu. Suna tattaruwa domin su yi yaki da wanda ke bisa doki da rundunarsa.
20 The Beast was captured, and with him was taken the false Prophet, who performed the marvels before the eyes of the Beast, with which he deceived those who had received the brand of the Beast and those who worshiped his image. Alive, they were thrown, both of them, into the fiery lake ‘of burning sulphur.’ (Limnē Pyr g3041 g4442)
Aka kama dabban tare da makaryatan annabawa da suka yi ayyukan al'ajibai a gabansa. Da wadannan alamu ya yaudari wadanda suka karbi alamar dabbar da wadanda suka yi wa siffarta sujada. Aka jefa dukansu biyu da rai cikin tafkin farar wuta mai ci. (Limnē Pyr g3041 g4442)
21 The rest were killed by the sword which came out of the mouth of him who rode upon the horse; and all the birds fed upon their flesh.
Sauran aka karkashe su da takobin da ke fitowa daga bakin mahayin dokin. Dukan tsuntsaye suka ci gawarwakinsu.

< Revelation 19 >