< Hebrews 6 >

1 Therefore, let us leave behind the elementary teaching about the Christ and press on to perfection, not always laying over again a foundation of repentance for a lifeless formality, of faith in God —
Saboda haka, sai mu ci gaba a kan ka'idodin farko na al'amarin Almasihu, har ya zuwa kammala, ba wai mu sake koyar da jigajigan nan na tuba da ibada marar tasiri ba, da na gaskatawa da Allah,
2 teaching concerning baptisms and the laying on of hands, the resurrection of the dead and a final judgment. (aiōnios g166)
da kuma na koyarwa a kan wanke-wanke, da dora hannu, da tashin matattu, da dawwamammen hukuci. (aiōnios g166)
3 Yes and, with God’s help, we will.
Za mu kuwa ci gaba in Allah ya yarda.
4 For if those who were once for all brought into the Light, and learned to appreciate the gift from Heaven, and came to share in the Holy Spirit,
Domin wadanda aka haskaka zukatansu sarai, har suka dandana baiwar nan Basamaniya, suka kuma sami rabo na Ruhu Mai Tsarki,
5 and learned to appreciate the beauty of the Divine Message, and the new powers of the Coming Age — (aiōn g165)
har su ka dandana dadin Maganar Allah, da ikon zamani mai zuwa, (aiōn g165)
6 if those, I say, fell away, it would be impossible to bring them again to repentance; they would be crucifying the Son of God over again for themselves, and exposing him to open contempt.
sa'an nan kuma suka ridda—ba mai yiwuwa ba ne a sake jawo su ga tuba, tun da yake sake gicciye Dan Allah suke yi su da kansu, suka kuma wulakanta shi a sarari.
7 Ground that drinks in the showers that from time to time fall upon it, and produces vegetation useful to those for whom it is tilled, receives a blessing from God;
Kasa ma da take shanye ruwan da ake yi a kai a kai, take kuma fid da tsire-tsire masu amfani ga wadanda ake nomanta dominsu, Allah yakan sa mata albarka.
8 but, if it ‘bears thorns and thistles,’ it is regarded as worthless, it is in danger of being ‘cursed,’ and its end will be the fire.
Amma idan tsire-tsirenta kaya ne da kashin yawo, ba ta da amfani ke nan, tana kuma gab da la'antarwa, karshenta dai konewa ne.
9 But about you, dear friends, even though we speak in this way, we are confident of better things — of things that point to your Salvation.
Ko da yake mun fadi haka, a game da ku kam, ya kaunatattu mun tabbata kuna abubuwa mafiya kyau na zancen ceto.
10 For God is not unjust; he will not forget the work that you did, and the love that you showed for his Name, in sending help to your fellow Christians — as you are still doing.
Gama Allah ba marar adalci ba ne, har da zai ki kula da aikinku, da kuma kaunar sunansa da kuke yi, wajen yi wa tsarkaka hidima, har yanzu ma kuna yi.
11 But our great desire is that every one of you should be equally earnest to attain to a full conviction that our hope will be fulfilled, and that you should keep that hope to the end.
Muna dai bukata kwarai kowannanku ya nuna irin wannan himma ga yin cikkaken bege, tabbatacce, har ya zuwa karshe.
12 Then you will not show yourselves slow to learn, but you will copy those who, through faith and patience, are now entering upon the enjoyment of God’s promises.
Don kada ku yi ragwanci, sai dai ku yi koyi da wadanda suka karbi cikar alkawaran nan, ta wurin bangaskiyarsu da hakurinsu.
13 When God gave his promise to Abraham, since there was no one greater by whom he could swear, he swore by himself.
Sa'adda Allah ya yi wa Ibrahim alkawari, da yake ba wani wanda ya fi shi girma da zai rantse da shi, sai ya rantse da kansa,
14 His words were — ‘I will assuredly bless thee and increase thy numbers.’
Ya ce, “Hakika zan yi maka albarka, in kuma ribambamya zuriyarka.”
15 And so, after patiently waiting, Abraham obtained the fulfilment of God’s promise.
Ta haka, Ibrahim bayan da ya jure da hakuri, ya karbi cikar alkawarin.
16 Men, of course, swear by what is greater than themselves, and with them an oath is accepted as putting a matter beyond all dispute.
Hakika mutane sukan rantse da abin da ya fi su. Rantsuwa kuma ita ce abar da take tabbatarwa da kowacce magana.
17 And therefore God, in his desire to show, with unmistakable plainness, to those who were to enter on the enjoyment of what he had promised, the unchangeableness of his purpose, bound himself with an oath.
Don haka, sa'adda Allah yake son kara tabbatar wa magadan alkawarin nan dahir, cewa nufinsa ba mai sakewa ba ne sam, sai ya hada da rantsuwa,
18 For he intended us to find great encouragement in these two unchangeable things, which make it impossible for God to prove false — we, I mean, who fled for safety where we might lay hold on the hope set before us.
Domin albarkacin abubuwa guda biyun nan marasa sakewa, masu nuna, cewa ba shi yiwuwa Allah ya yi karya, mu da muka gudu muka sami mafaka, mu karfafa kwarai mu riski abin da muka kafa bege a kai.
19 This hope is a very anchor for our souls, secure and strong, and it ‘reaches into the Sanctuary that lies behind the Curtain,’
Muna da bege, kamar yadda yake ga rai, kafaffe, tabbatacce, shi ne kuma yake shiga har can ciki bayan labulen.
20 where Jesus, our Forerunner, has entered on our behalf, after being made for all time a High Priest of the order of Melchizedek. (aiōn g165)
Inda saboda mu ne Yasu ya riga mu shiga, da yake ya zama Babban Firist na har abada, kwatancin Malkisadak. (aiōn g165)

< Hebrews 6 >