< Psalms 81 >

1 Sing [songs] to praise God, who enables us to be strong [when we fight our enemies]; shout joyfully to God, whom we (descendants of Jacob/Israeli people) [worship]!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Start [playing] the music, and beat the tambourines, and play nice music on the harps and (lyres/other stringed instruments).
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Blow the trumpets [during the festival to celebrate] each new moon and each time the moon is full and during our [other] festivals.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 [Do that] because that is a law for [us] Israeli [people]; God commanded it for us descendants of Jacob.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 He commanded us Israeli [people to obey it] when he punished [the people of] Egypt. I heard someone [MTY] whose voice I did not recognize, saying,
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 “[After the rulers of Egypt forced you Israelis to work as slaves], I took those [heavy] burdens off your backs, and I enabled you to lay down those [heavy] baskets [of bricks that you were carrying].
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 When you were [greatly] distressed, you called [out to me], and I rescued you; I answered you out of a thundercloud. [Later] I tested [whether you would trust me to give you] water [when you were in the desert] at Meribah.
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 [You who are] my people, listen while I warn you! I wish that you Israeli [people] would pay attention to what I [say to you]!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 You must not have any idols of other gods among you; you must never bow to worship any of them!
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 I am Yahweh, your God; It was [not any of those other gods] who brought you out of Egypt, I am the one who did it! [So] ask me what you want me to do for you [MTY], and I will do it.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 But my people would not listen to me [SYN]; they would not obey me.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 So even though they were very stubborn, I allowed them to do whatever they wanted to do.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 I wish that my people would listen to me, that the Israeli [people] would behave as I want them to do.
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 [If they did that], I would quickly defeat their enemies; I would strike/punish [all of] them [DOU].
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 [Then all] those who hate me would (cringe before/bow down to) me, and [then I] would punish them [MTY] forever.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 [But] I would give you [Israelis] very good wheat/grain, and I would fill your stomachs with wild honey.”
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”

< Psalms 81 >