< Psalms 44 >

1 God, we ourselves have heard what our parents and grandparents told us. They told us about the miracles that you performed long ago.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 [They told us] how you expelled the ungodly people and enabled us to live in their land. [They told us] that you punished those ungodly people and enabled your own people to prosper [IDM].
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 It was not by using their own swords that they conquered the people that lived in that land, and it was not by their own power that they were victorious; it was only by your power [MTY, DOU] [that they did those things]; and they were sure that you were with them, and that showed that you were pleased with them.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 You are my King and my God; it is you who enable us, your people [MTY], to defeat our enemies.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 It is by your power that we knock our enemies down and tramp on them.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 I do not trust that I will be saved by using my bow [and arrows] and my sword.
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 No, it is you who have rescued us from our enemies, it is you who have caused those who hate us to become ashamed [because they were defeated].
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 We have continually boasted about what God [has done for us], and we will thank him [MTY] forever.
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 But [now] you have rejected us and caused us to be disgraced; when our armies march out [to fight a battle], you no [longer] go with them.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 You have caused us to run away from our enemies, with the result that they captured the things that belonged to us.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 You have allowed us to become like [MET] sheep that were ready to be slaughtered; you scattered us [far away] among [other].
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 [It is as though] [MET] you sold us, your people, [to our enemies] for a very small price, and you did not gain much profit from selling us!
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 People who live in nations near us make fun of us; they laugh at us and deride/belittle us.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 They make jokes using the name of [our country], they shake their heads [to indicate that they despise us].
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 All day I feel disgraced; from seeing my face, people know that I am ashamed.
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 I hear what those who sneer at me and revile me say; I am ashamed in front of my enemies and those who want to harm me.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 All these things have happened to us [even] though we have not forgotten you, and we are not the ones who disobeyed the agreement you made with [our ancestors].
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 We have not stopped being loyal to you, and we have not stopped doing what you want us to do [IDM].
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 But [it is as though] you have allowed us to be helpless among wild animals, and abandoned us in a deep dark [ravine].
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 If we had forgotten to worship [MTY] our God, or if we had spread out our hands to [worship] a foreign god,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 you certainly would have known that, because you know [even] what we secretly think.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 But it is because we belong to you, [that our enemies] are constantly killing us. They act toward us as though we were only sheep to be slaughtered.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 [So], Yahweh, arise! Why are you asleep [RHQ]? Get up! Do not reject us forever!
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Why are you not looking at us? Why are you forgetting that we are suffering and being oppressed [by our enemies]?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 We are pushed down to the ground and we cannot get up.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Arise, and come and help us! Rescue us because you faithfully love us!
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.

< Psalms 44 >