< Psalms 17 >

1 Yahweh, listen to me while I plead with you to act justly toward me. Hear me while I call out to you to help me. Pay attention to what I say while I pray because I am speaking [MTY] honestly/truthfully.
Addu’a ce ta Dawuda. Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.
2 You are the one who is able to declare that I (am innocent/have not done anything that was wrong) because you see/know that I am telling the truth.
Bari fiffitawata tă zo daga gare ka; bari idanunka su ga abin da yake daidai.
3 You know what I think, [even] at night; you have examined what I say and do, and you know that I have determined to never tell any lies.
Ko ka duba zuciyata, ka kuma bincike ni da dare, ko ka gwada ni, ba za ka sami kome ba; na yanke shawara cewa bakina ba zai yi zunubi ba.
4 I have not done like others do; I have always done what is right [IDM], and I have not acted cruelly toward others.
Game da ayyukan mutane kuwa, ta wurin maganar leɓunanka na kiyaye kaina daga hanyoyin tashin hankali.
5 I have always done what you told me to do [IDM], I have (never failed to do/always done) [LIT] those things.
Sawuna sun kama hanyoyinka ƙafafu kuwa ba za su yi santsi ba.
6 O God, I pray to you because you answer me; please listen [MTY] to what I am saying.
Na kira gare ka, ya Allah, gama za ka amsa mini; ka kasa kunne ka kuma ji addu’ata.
7 Show me that you faithfully love me. By your great power [MTY] rescue those who (run to/trust in) you to protect them from their enemies.
Ka nuna mini girmar ƙaunarka mai banmamaki, kai da kake ceton waɗanda suke neman mafaka daga abokan gābansu da hannunka na dama.
8 Protect me as people carefully protect their own eyes; protect me like [birds] protect [their babies] under their wings [MET].
Ka kiyaye ni yadda ake kiyaye ido; ka ɓoye ni cikin inuwar fikafikanka
9 Do not allow wicked people to attack me; my enemies surround me, wanting to kill me.
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10 They never pity [IDM] anyone, and they are always boasting.
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11 They have hunted/searched for me and found me. They surround me, watching for an opportunity to throw me to the ground.
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12 They are like lions [SIM] that are ready to tear apart the animals that they capture; they are like young lions that are hiding, waiting to pounce [on their prey].
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13 Yahweh, come and (oppose/fight against) my enemies and defeat them! Use your sword to save me from those wicked people!
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14 Yahweh, by your power [MTY] rescue me from those people who are interested [only] in things here in this world. But you provide plenty of food for those whom you love dearly; their children also have many things that their grandchildren will inherit.
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so;’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa’ya’yansu.
15 Yahweh, because I act righteously, I will [some day] see you [SYN]. When I awake, I will see you face-to-face, and then I will be happy.
Amma ni, cikin adalci zan ga fuskarka; sa’ad da na farka, zan gamsu da ganin kamanninka.

< Psalms 17 >