< Numbers 31 >

1 Yahweh spoke to Moses/me and said,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Before you die, [tell the] Israeli people that they should (pay back/get revenge on) the Midian people-group for what they did to you.”
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 So Moses/I said to the people, “Get some men prepared for battle. Yahweh will enable them to (pay back/get revenge on) the Midian people-group [for what they did to us].
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4 Select 1,000 men from each tribe to fight.”
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5 So 12,000 men prepared for fighting in the battle, 1,000 from each tribe.
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6 When Moses/I sent them to the battle, Phinehas, the son of Eleazar the priest, went with them. He took with him some of the things from the Sacred Tent and the trumpets that would be blown to give the signal [to start the battle].
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
7 The Israeli men fought the soldiers from the Midian people-group, as Yahweh had told Moses/me to tell them to do, and they killed every man from the Midian people-group.
Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
8 Among those whom they killed were the five kings of the Midian people-group—Evi, Rekem, Zur, Hur, and Reba. They also killed with a sword Balaam, the son of Beor.
A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
9 They captured all the women and children of the Midian people-group and took away their cattle, their flocks of sheep, and herds of goats, and all their other possessions.
Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
10 Then they burned down all the houses in the towns and villages where the people of the Midian people-group lived,
Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
11 but they took home with them all the women and children and animals and possessions.
Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
12 They brought all these to Eliezer and Moses/me, and to the rest of the Israeli people who were at their/our camp on the plains where the Moab people-group lived, near the Jordan River, across from Jericho.
suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
13 Eleazar and all the leaders of the people and Moses/I went outside the camp to greet/meet with them.
Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
14 But Moses/I was angry with some of the men who had returned from the battle. He/I was angry with the army officers and the men who were commanders of 1,000 men and those who were commanders of 100 men.
Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
15 He/I asked them, “Why did you allow the women to live [RHQ]?
Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
16 They are the ones who did what Balaam suggested and urged/persuaded our people to worship Baal [instead of Yahweh]. As a result, Yahweh caused a plague to strike his people while they were at Peor.
Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
17 So, now you must kill all the boys of the Midian people-group, and also kill all the women who have had sex [EUP] with any man.
Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
18 Spare only the girls who are virgins [EUP]. You can keep them to be your [wives or your slaves].
amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
19 All of you who have killed someone or touched the corpse of someone who was killed [in the battle] must stay outside the camp for seven days. On the third day and on the seventh day, you must [perform the ritual to] cause you and those whom you have captured to become acceptable to God again.
“Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
20 You must also wash your clothes and anything [that you took to the battle] that is made of leather or goat’s hair or wood.”
Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
21 Then Eleazar said to the soldiers who had returned from the battle, “This is what Yahweh has instructed Moses:
Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
22 You must put into a fire any gold or silver or bronze or iron or tin or lead things [that you brought back from the battle].
Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
23 Put everything that will not burn into the fire, and then they will be acceptable for you to use. But also sprinkle those things with the water that causes things and people to become acceptable to God. The things that would burn [if you put them] in a fire, sprinkle them with that water.
da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 On the seventh day, wash your clothes, and then you will become acceptable to God again. After you do that, you may return to the camp.”
A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
25 Yahweh also said to Moses/me,
Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
26 “Tell Eleazar and the leaders of the family groups that they must write down a list of all the goods, the women, and the animals that were captured [in the battle].
“Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
27 Then they must divide all those things, half given to the men who fought in the battle and the other half given to the rest of the people.
Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
28 From the men who fought in the battle, take one from every 500 people and from every 500 cattle and donkeys and sheep, to be a tax for me.
Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
29 Take these things to Eleazar to (be my share/belong to me).
Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
30 And from the half that belongs to the ordinary people, take one item from every 50. That includes people, cattle, donkeys, sheep, goats, and other animals. Give those things to the descendants of Levi who take care of my Sacred Tent.”
Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
31 So Eleazar and Moses/I did what Yahweh commanded.
Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
32 There were 675,000 sheep, 72,000 cattle, 61,000 donkeys, and 32,000 virgins that they had captured from the Midian people-group.
Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
shanu 72,000
da jakuna 61,000.
Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
36 The men who fought in the battle took 337,000 sheep [from the battle],
Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
37 and they gave 675 of them to Yahweh.
tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
38 They took 36,000 cattle and gave 72 of them to Yahweh.
shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
39 They took 30,500 donkeys, and they gave 61 of them to Yahweh.
jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
40 They took 16,000 virgins, and they dedicated 32 of them to Yahweh.
mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
41 Moses/I gave to Eleazar all [the animals] that had been given to Yahweh, as Yahweh had commanded.
Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
42 Moses/I separated what those who had fought in the battle received from what the other people received. The people had taken 337,500 sheep, 36,000 cattle, 30,500 donkeys, and 16,000 virgins,
Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
shanu 36,000,
jakuna 30,500
da mutane 16,000.
47 From what the people received, Moses/I took one from every 50 items and dedicated them to Yahweh. That included animals and people. As Yahweh commanded, he/I gave them all to the descendants of Levi who took care of the Sacred Tent.
Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
48 Then the army officers and those who commanded 1,000 men and those who commanded 100 men came to Moses/me.
Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
49 They said, “We, who are your servants, have counted the soldiers whom we command, and [we found that] none of them (is missing/has been killed).
suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
50 So [to thank Yahweh for that], we have brought to him a gift of the gold items that we found [after the battle]: Gold arm bands and bracelets and rings and earrings and necklaces. This will enable us to be forgiven for our sins.”
Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
51 So Eleazar and Moses/I accepted the gold items that they brought.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
52 The total of it weighed about (420 pounds/190 kg.).
Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
53 Each soldier had taken these things for himself.
Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
54 Eleazar and Moses/I accepted these gold items from these commanders and put them in the Sacred Tent to remind the Israeli people about how Yahweh [had helped them defeat the Midian people-group].
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.

< Numbers 31 >