< Numbers 13 >

1 Yahweh said to Moses/me,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Send some men to Canaan [land] to explore it. That is the land that I will give to you Israelis. Send men who are leaders in their tribes.”
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 So Moses/I did what Yahweh commanded him/me. He/I sent out twelve Israeli men who were all leaders of their tribes. He/I sent them from their/our camp at Paran in the desert.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 These are the names of the men [and the tribes they belonged to: ] Shammua, the son of Zaccur, from the tribe of Reuben;
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 Shaphat, the son of Hori, from the tribe of Simeon;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 Caleb, the son of Jephunneh, from the tribe of Judah;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 Igal, the son of Joseph, from the tribe of Issachar;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 Hoshea, the son of Nun, from the tribe of Ephraim;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 Palti, the son of Raphu, from the tribe of Benjamin;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 Gaddiel, the son of Sodi, from the tribe of Zebulun;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 Gaddi, the son of Susi, from the tribe of Manasseh;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 Ammiel, the son of Gemalli, from the tribe of Dan;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 Sethur, the son of Michael, from the tribe of Asher;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 Nahbi, the son of Vophsi, from the tribe of Naphtali;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 and Geuel, the son of Maki, from the tribe of Gad.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 Those are the names of the men whom Moses/I sent out to explore Canaan. [Before they left], Moses/I gave Hoshea a new name, Joshua, [which means ‘Yahweh is the one who saves].’
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Before Moses/I sent them to explore Canaan, he/I said to them, “Go through the southern part of Canaan, and then go [north] into the hilly area.
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 See what the land is like. See if the people who live there are strong or weak. See if there are many people or only a few people.
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 Find out what kind of land they live in [RHQ]. Is it good or bad? Find out about the towns in which they live [RHQ]. Do they have walls around them or not?
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 Find out about the soil [RHQ]. Is it (fertile/good for growing crops) or not? Find out if there are trees there [RHQ]. Try to bring back some of the fruit that grows in that land.” [He/I said that because] it was the beginning of the time to harvest grapes.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 So those men went to Canaan. They went [through the entire land], from the Zin desert [in the south] all the way to Rehob [town] near Lebo-Hamath [in the north].
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 In the south, they went to Hebron, where Ahiman, Sheshai, and Talmai, [huge men] descended from Anak, lived. Hebron was a city that was built seven years before Zoan [city] was built in Egypt.
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 In one valley, they cut from a grapevine one cluster of grapes. [Because it was very large, they needed] two men to carry it on a pole. They also picked some pomegranates and some figs [to carry back to their camp].
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 They called that place Eshcol [which means ‘cluster’] because they had cut that [huge] cluster of grapes there.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 After they explored the land for 40 days, they returned to their camp.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 They came to Aaron and Moses/me and the rest of the Israeli people in the desert at Paran. They reported to everyone what they had seen. They also showed them the fruit that they had brought back.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 But this is what they reported to Moses/me: “We arrived in the land that you sent us to explore. It is truly a beautiful land, and it is very fertile [IDM]. Here is some of the fruit.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 But the people who live there are very strong. Their cities are large and are surrounded by walls. We even saw some of the [huge] descendants of Anak there.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 The descendants of Amalek live in the southern part [of the land], and the descendants of Heth, Jebus, and Amor live in the hilly area [to the north]. The descendants of Canaan live along the coast of the [Mediterranean] sea and along the Jordan [River].”
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 [When they said that, the people were afraid and started to cry out very loudly]. But Caleb told the people who were standing near Moses/me to be quiet. Then he said, “We should go there and take the land, because we are certainly able to conquer it!”
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 But the men who had gone with him said, “No, we cannot attack [and defeat] those people! They are much stronger than we are!”
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 So those men gave to the Israeli people a bad report about the land that they had explored. They said, “The land that we explored is very large; we cannot conquer it. And all the people whom we saw are very tall.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 We even saw the descendants of Nephili there. The descendants of Anak [whom we saw there] are descended from the giant Nephili people. When we saw them, we felt [as small] as grasshoppers [SIM], and they thought that we looked like grasshoppers too!”
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Numbers 13 >