< Luke 14 >

1 One (Jewish day of rest/Sabbath day), Jesus went to eat [SYN] at the house of an important Pharisee. Some [men who studied the Jewish] laws and other Pharisees who were there were watching him carefully [to see if he would do something for which they could accuse him].
Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
2 Unexpectedly, there was a man in front of Jesus whose arms and legs were swollen.
A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
3 Jesus said to them, “Is it permitted in [our(inc)] Jewish laws to heal [someone] (on our Jewish rest day/on the Sabbath), or not?”
Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
4 [They knew that their laws permitted it, but they thought that healing was work, which they thought was wrong to do] (on the Sabbath/on the Jewish rest day) (OR, [they knew that their laws permitted it, but they did not want to admit it]). So they did not reply. Then Jesus put his hands on the man and healed him. Then he told him to go [home].
Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
5 Then he said to the rest of them, “If you had a son or an ox that fell into a well on a (Sabbath/our day of rest), would you immediately [work to] pull him out, [or would you(sg) let him stay there until the next day]?”
Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
6 [They knew that they would immediately work to pull him out, even on their day of rest, so they could not justly say that Jesus did wrong by healing the man on that day. So] they said nothing in reply to Jesus.
Suka rasa abin faɗi.
7 Jesus noticed that those people who had been {whom [the Pharisee] had} invited [to the meal] chose [to sit in] the places where important [people usually sit]. Then he gave [this advice] to them:
Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
8 “When one of you [(sg)] is invited by someone {someone invites one of you [(sg)]} to a wedding feast, do not sit in a place where important people sit. Perhaps the man [giving the feast] has invited a man more important than you [(sg)].
“In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
9 [When that man comes], the man who invited both of you will come to you [(sg)] and say to you, ‘Let this man take your seat!’ Then you [(sg)] will have to take the most undesirable seat, and you will be ashamed.
In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
10 Instead, when you are invited {[someone] invites one of you} [to a feast], go and sit in the most undesirable seat. Then when the man who invited everyone comes, he will say to you [(sg)], ‘Friend, sit in a better seat!’ Then all the people who are eating with you [(sg)] will see that he is honoring you.
Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
11 Also, [remember this]: [God] will humble those who exalt themselves. And [he] will exalt those who humble themselves.”
Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
12 [Jesus] also said to [the Pharisee] who had invited him to the meal, “When you [(sg)] invite people to a midday or evening meal, do not invite your friends or your family or your other relatives or your rich neighbors. They can later invite you [(sg) for a meal]. In that way they will repay you.
Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
13 Instead, when you [(sg)] give a feast, invite poor [people], crippled [people], lame [people], or blind [people].
Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
14 They will be unable to repay you. [But God will bless you! He] will repay you [at the time] when [he causes] righteous people to become alive again.”
Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
15 One of those who were eating with Jesus heard him say that. He said to Jesus, “God [has truly] blessed [us Jews] who will eat [with the Messiah] when he starts to rule!”
Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
16 But [to show that many Jews whom God had invited would not accept God’s invitation] [MET], Jesus replied to him, “One time a man [decided] to prepare a large feast. He invited many people to come.
Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
17 When it was the day for the feast, he sent his servant to tell those who had been {whom he had} invited, ‘Come [now] because everything is ready!’
Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
18 But [when the servant did that], all of the people [whom he had invited] began to say why they did not want to come. The first [man the servant went to] said, ‘I have just bought a field, and I must go and see it. Please [ask your master to] forgive me for not coming!’
“Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
19 Another person said, ‘I have just bought five pair of oxen, and I must go to examine them. Please [ask your master to] forgive me for not coming!’
“Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
20 Another person said, ‘I have just been married. So I cannot come.’
“Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
21 So the servant returned to his master and reported what [everyone had said]. The owner of the house was angry [when he heard the reasons they gave for not] coming. He said to his servant, ‘Go out quickly to the streets and alleys of the city [and find] poor and crippled and blind and lame [people, and bring] them here into [my house]!’
“Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
22 [After the servant went and did that], he [came back and] said, ‘Sir, I have done what you [(sg)] told me to do, but there is still room [for more people].’
“Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
23 [So] his master said to him, ‘Then go [outside the city]. Search for people along the highways. Search also along the narrow roads with hedges beside them [where homeless people may be staying]. Strongly urge the people in those places to come to [my house]. I want it to be full of [people]!’”
“Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
24 [Then Jesus said], “I tell you [(pl)] this: Very few of you [Jewish] people will enjoy my feast, even though [I] invited you [first to eat it with me when I become king].”
Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
25 Large groups of people were traveling with [Jesus]. He turned and said to them,
Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
26 “If anyone comes to me who loves his father and mother and wife and children and brothers and sisters [more than] [HYP] [he loves me], he cannot be my disciple. He must even love me more than he loves his own life!
“Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
27 [People who are ready to execute a prisoner make] him carry his cross [MET] [to the place where others will nail him] on it. Only those who are willing [to allow others to hurt them and disgrace them] like that because of being my disciples, and who are willing to obey what I teach, can be my disciples.
Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
28 [I will illustrate] [MET]. If one of you desired to build a (tower/big house), (you would surely first sit down and determine how much it would cost!/would you not first sit down and determine how much it would cost?) [RHQ] Then you would determine whether you had enough money to complete it.
“In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
29 [If you did not do that], if you laid the foundation and were not able to finish [the rest of the tower], everyone who saw it would make fun of you.
Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
30 They would say, ‘This man started to build [a tower], but he was not able to finish it!’
yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
31 Or, if a king decided to [send his army to] war against another king, (he would surely first sit down [with those who] advised [him]./would he not first sit down [with those who] advised [him]?) [RHQ] They would determine whether [his army], which had only 10,000 soldiers, could defeat the [other army], which had 20,000 soldiers, and was about to attack his [army].
“Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
32 If he [decided] that his army could not [defeat that army], he would send messengers to [the other king] while the other army was still far away. He would tell the messengers to say to that king, ‘What things must I do to have peace with your country?’
In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
33 So, similarly, if any one of you does not first decide that you [(sg)] are [willing to] give up all that you have, you cannot be my disciple.”
Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
34 [Jesus also said, “You are like] [MET] salt, which is useful [to put on food]. But (salt certainly cannot be made {[you] certainly cannot make salt} to taste salty again if it stops tasting salty!/can salt be made {can [you] make salt} to taste salty again if it quits tasting salty?) [RHQ]
“Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
35 [If salt does not taste salty any more], it is not good for the soil or even for the manure heap. [People] throw it away. [The same thing will happen to you if you become useless to God]. If you want to understand what I just said [IDM], you must consider [carefully] what you have heard!”
Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

< Luke 14 >