< Luke 1 >

1 My noble [friend] Theophilus, many people saw the things that [Jesus] did while he was with us, from the time when he started [MTY] [his ministry]. They served God [by teaching people] the message [about the Lord Jesus]. Many of those who heard what they taught wrote down for us accounts of the things that [Jesus did from the time when] he began [his ministry].
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 I myself have studied these accounts carefully. So I decided that it would be good for me also to write for you [(sg)] an accurate account of these matters.
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 I want you to know the truth about what you have been taught {what others have taught you}.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 When King Herod [the Great ruled] Judea [district], there was a [Jewish] priest named Zechariah. He belonged to the [group of priests called] the Abijah group. He and his wife Elizabeth were both descended from the [first priest of Israel], Aaron.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 [God considered that] both of them were righteous, because they constantly completely obeyed everything that God had commanded.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 But they had no children, because Elizabeth had been unable to bear children. Furthermore, she and her husband were very old.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 One day [Zechariah’s] group was doing their work [in the Temple in Jerusalem], and he was serving as a priest in God’s presence.
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Following their custom, [the other priests] chose him by lot to enter the Lord’s temple and burn incense.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 While he was burning the incense, many people were outside [in the courtyard], praying.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Then an angel whom God had [sent] appeared to him. The angel was standing at the right side of the place [where the priests burned] incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 When Zechariah saw the angel, he was startled and became very afraid.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him, “Zechariah, do not be afraid! When you [(sg)] prayed [asking God for a son] (OR, [that God would send the Messiah]), God heard what you prayed. [So] your wife Elizabeth shall bear a son. You must name him John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 He will cause you to be very happy, and many other people will also be happy because he is born.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 God will consider him to be very important. He must never drink wine or any other alcoholic drink, [in order that he will be completely dedicated to God]. He will be controlled by the Holy Spirit {The Holy Spirit will control him} from before he is born.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 He will [persuade] many people in Israel to turn away [from their sins and please] the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 As [God’s] Spirit enables him [to preach] powerfully as [the prophet] Elijah did, he will precede [the Messiah]. He will cause parents [SYN] to act [peacefully] toward their children [again]. He will cause [many] people who do not obey [God to hear and obey] the wise things that righteous people [tell them]. He will do this in order to help [many] people to be ready when the Lord [comes].”
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Then Zechariah said to the angel, “I am very old, and my wife is also so old [that she cannot bear a child. So] (I cannot [believe] that what you [(sg)] said [will happen]!/how can I [believe] that what you [(sg)] said [will happen]?) [RHQ]”
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Then the angel said to him, “I am [God’s chief angel], Gabriel! [I do what God tells me, because] I constantly am in God’s presence! I was sent {[He] sent me} to tell you [(sg)] something good [that is going to happen to you].
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 What I have told you will certainly happen at the time [God decides], but you did not believe what I told you. So now [God will make] you will be unable to talk until the day [your son is born]”!
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 While [Zechariah and the angel] were talking, the people [in the courtyard] were waiting for Zechariah [to come out]. They wondered, “Why is he staying in the Temple for such a long time?”
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 When Zechariah came out, he was not able to speak to the people. Because he could not talk, he made motions with his hands [to try to convey what had happened]. Then they realized that he had seen (a vision [from God]/something that [God] showed him) while he was in the Temple.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 When Zechariah’s time to work [as a priest in the Temple] was finished, he [left Jerusalem and] returned to his home.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Some time later his wife Elizabeth became pregnant [EUP]. She did not leave their house for five months, [because she knew that people would laugh at her if she told them that she was pregnant].
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 But she thought, “God has enabled me to become pregnant. He has pitied me and I will no longer be ashamed [because I have no children]!”
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 When Elizabeth had been [pregnant] [EUP] [for almost] six months, the angel Gabriel was sent by God {God sent the angel Gabriel} [again].
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 [This time] he went to Nazareth [town] in Galilee [district], to a virgin whose name was Mary. It had been {[Her parents] had} promised that she would marry a man named Joseph, who was descended from [King] David.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 The angel greeted her and said, “(The Lord/God) is with you [(sg)] and you will be greatly blessed {[has decided to] greatly bless you}!”
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But Mary was very confused [when she heard] that. She wondered what [the angel meant] by these words.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Then the angel said to her, “Mary, God is very pleased with you [(sg)], so do not be afraid.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 You will become pregnant and bear a son, and you must name him Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will become great. He will be called {[People will] call him} (the Son of God/the man who is also God). God, the Lord, will make him a king [MTY] as his ancestor [King] David was.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 He will be the King of [the] Jews, the descendants [MTY] of [your ancestor] Jacob, forever. He will rule as king forever!” (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Then Mary said to the angel, “I am a virgin, so how can I [have a baby]?”
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 The angel replied, “The Holy Spirit will come to you; the power of God [MTY/EUP] will overshadow you [and enable you to become pregnant]. So the child [you will] bear will be completely set apart {give himself completely} to obey God, and he will be called {[people] will say that he is} (the Son of God/the man who is also God).
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 [I also need to tell you something else]. Your cousin Elizabeth is very old, and it was thought {[people] said} that she could not bear any children. But she has been [pregnant] [EUP] [for almost] six months, and will bear a son!
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 [You should not be surprised at that], because God can do everything!”
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Then Mary said, “All right, I want to serve (the Lord/God), so may what you [(sg)] have said about me come true!” Then the angel left her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Very soon after that, Mary got ready and went quickly to a town in the highlands of Judea [district] where Zechariah lived.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 She entered his house and greeted [his wife] Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 As soon as Elizabeth heard Mary greet her, the baby moved inside [Elizabeth’s] womb. The Holy Spirit took complete control of Elizabeth,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and she said loudly [to Mary], “[God] has blessed you [more than] he has blessed [any other] woman, and [he has] blessed the child you will bear!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 (I am not worthy that [God would allow you] to visit me!/Why is [God allowing you] to visit me?) [RHQ] You will be the mother of my Lord!
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 [I realize this because] as soon as I heard you greet me, the baby inside my womb moved because he was so happy [that you had come].
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 [God] is pleased with you [because] you believed that what (the Lord/God) told you would come true.”
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Then Mary [praised God by] saying/singing: “, how I [SYN] praise (the Lord/God)!
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 I am happy because God is the one who saves me.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 I was only his lowly servant girl, but he did not forget me. So from now on, everyone will say that God was pleased with me,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 because they will hear about the things that God [MTY], the mighty one, has done for me. He [MTY] is awesome!
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 He acts mercifully toward all those who respect him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He shows people that he [MTY] is very powerful. He scatters those who think proudly.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He does not let mighty kings rule [MTY] any more, but he honors people who are oppressed (OR, humble).
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He gives good things to eat to those who are hungry, but he sends away the rich people without giving them anything.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 And now he has remembered what he promised. So he has helped me and all the other people of [MTY] Israel who serve him.
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 He promised to Abraham and all our other ancestors who descended from him that he would act mercifully toward them forever.” (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Mary stayed with Elizabeth for about three months. Then she returned to her home.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 When it was time for Elizabeth to give birth to her child, she bore a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Her neighbors and relatives heard how (the Lord/God) had greatly blessed her [by enabling her to bear a child], so they were happy along with [Elizabeth].
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Seven days later they gathered together for the [ceremony for] circumcising the baby [to show that he belonged to God]. They wanted to give the baby the same name as his father, Zechariah.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 But his mother said, “No, [his name will not be Zechariah]. His name will be John!”
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 [So] they said to her, “[John] is not the name of any of your [(dl)] relatives, [so you(dl) should not give him that name]!”
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Then they made motions with their hands to Zechariah, [for him] to indicate what name [he] wanted to be given {to give} to his son.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 [So] he signaled that they [should give him] a tablet [to write on. When they gave him one], he wrote [on it], “His name is John.” All those [who were there] were surprised!
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Immediately Zechariah was able to speak again [MTY], and he praised God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 All their neighbors were amazed/awestruck! They told other people who lived all over the highlands of Judea about what had happened.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Everyone who heard about it kept thinking about it. They were saying, “We wonder what will this child do [for God when] he [grows up] [RHQ]!” They wondered that because [from what had happened they were sure that] God would be helping that child [SYN] [in a powerful way].
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 [After] Zechariah’s [son was born], Zechariah was completely directed by the Holy Spirit {the Holy Spirit completely directed Zechariah} as he spoke these words that came from God:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 “Praise the Lord, the God whom we(inc) people of Israel worship, because he has come to set us, his people, free from our enemies.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 He is sending us someone who will powerfully [MTY] save us, someone who is descended from [MTY] King David, who served God well.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Long ago God caused his prophets to say that he would do that. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 He will rescue us from our enemies, and he will save us from the power of all those who hate us.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 He will do this because he has not forgotten what he promised our ancestors; he made an agreement that he would act mercifully to us, their descendants.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 That is what he strongly promised our ancestor Abraham that he would do.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 God told him that we would be rescued {he would rescue us} from the power of our enemies, that he would enable us to serve him without being afraid,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 that he would cause us to be completely dedicated to him, and enable us to live righteously all of our lives.”
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 [Then Zechariah said this to] his little son: “My child, you will be called {people will say that you are} a prophet whom God [MTY/EUP] has sent; you will begin your work before (the Lord/Messiah) comes; you will prepare people so that they will be ready for him. (OR, you will begin your work before the Messiah comes).
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 You will tell God’s people how he will forgive them and save them from being punished for their sins.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Our God will do that because he is very kind to us. Just like a new day begins when the sun rises [MET], God will do that new thing for us when the Messiah comes to us from heaven.
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 People who do not know God [MET] are like those who sit in the darkness. They are afraid [MTY] that they will soon die. But when the Messiah tells us God’s message, it will be like causing such people to see a bright light. He will guide us [SYN] so that we will be living peacefully.”
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 [Later], Zechariah’s son grew up and became spiritually strong. Then he lived in a desolate region until he began to preach to the Israeli people.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >