< Judges 16 >

1 One day Samson went to Gaza [city in the Philistia area]. He spent some time with a prostitute.
Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
2 People soon found out that Samson was there, so the men of Gaza gathered together at the city gate and waited all night. They said to themselves, “When it dawns tomorrow morning, we will kill him [when he tries to leave the city].”
Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
3 But Samson did not stay there all night. At midnight, he got up. He went to the city gate, he took hold of its two posts, and he lifted it up out of the ground, with its [connecting cross] bar still attached. He put it on his shoulders and carried it [many miles] uphill to Hebron.
Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
4 Later Samson fell in love with a woman named Delilah, [and started to live with her]. She lived in Sorek Valley [in the Philistia area].
Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
5 The Philistine leaders went to her and said, “Find out from Samson what makes him so strong. And find out how we can subdue him and tie him up securely. If you do that, each of us will give you 1,100 pieces of silver.”
Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
6 So Delilah said to Samson, “Please tell me what makes you so strong, and tell me how someone can subdue you and tie you up.”
Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
7 Samson said, “If someone ties me with seven new bowstrings, ones that are not dry yet, I will become as weak as other men.”
Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
8 So [after Delilah told that to the Philistine leaders], they brought seven new bowstrings to Delilah.
Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
9 Then she hid the men in one of the rooms in her house. Then [while Samson was sleeping], she tied him up with the bowstrings. Then she called out, “Samson! The Philistines have come here to capture you!” But Samson snapped the bowstrings as easily as though they were strings that had been singed in a fire. So the Philistines did not find out what made Samson so strong.
Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
10 Then Delilah said to Samson, “You have deceived me and lied to me! Now tell me [the truth, ] how someone can tie you up securely.”
Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
11 Samson replied, “If someone ties me with new ropes, ones that have never been used, I will be as weak as other men.”
Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
12 So again, [she told the Philistine leaders, and] they [came and] hid in the room as they had done before. And again, while Samson was sleeping, she took the new ropes and tied him up with them. Then she called out, “Samson! The Philistines have come to capture you!” But Samson snapped the ropes on his arms as easily as if they were threads.
Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
13 Then Delilah said, “You have deceived me and lied to me [again]! Please tell me how someone can tie you up securely!” Samson replied, “If you weave the seven braids of my hair into the threads you are weaving on the loom, and then fasten those threads with the pin [that makes the threads tight], then I will be as weak as other men.” So again, while Samson was sleeping on her lap, Delilah held the seven braids of his hair, and wove them into the threads on the loom,
Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
14 and she tightened them with the pin. Then she called out, “Samson! The Philistines have come to capture you!” But Samson woke up and pulled out the pin, and pulled his hair from the threads on the loom.
ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
15 Then Delilah said to him, “How can you say that you love me when you do not tell me the truth about yourself? You have deceived me three times, and you still have not told me what really makes you so strong!”
Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
16 Day after day she nagged him like that. He thought he would die from her nagging [IDM].
Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
17 Finally Samson told her the truth. He said, “I have been set apart for God since the day I was born. And because of that, my hair has never been cut. If my hair were shaved off, my strength would be gone, and I would be as weak as other men.”
Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
18 Delilah realized that this time he had told her the truth. So she summoned the Philistine leaders again, saying, “Come back one more time, because Samson has really told me everything [about why he is so strong]”. So the Philistine leaders returned and brought to Delilah the money [that they promised to give her].
Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
19 Again she lulled Samson to sleep, with his head in her lap. Then she called one of the Philistine men to come and shave off Samson’s hair. As he did that, Samson began to get weaker. And finally his strength was all gone.
Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
20 Then [after she tied him up], she called out, “Samson! The Philistines have come to capture you!” He woke up and thought, “I will do as I did before. I will shake [these ropes] off myself and be free!” But he did not realize that Yahweh had left him.
Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
21 So the Philistine men seized him and gouged out his eyes. Then they took him to Gaza. There they put him in prison and bound him with bronze chains. They made him [turn a millstone to] grind grain [every day].
Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
22 But his hair started to grow again.
Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
23 [Several months later] the Philistine leaders celebrated a big festival. During the festival they offered sacrifices to their god Dagon. They praised him, saying, “Our god has enabled us to defeat our great enemy Samson!”
To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
24 And when the other people saw Samson, they also praised their god Dagon, saying, “Samson ruined our crops and killed many of our people, but our god has put our enemy into our hands. Our god helped us to capture the one who has killed so many of us!”
Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
25 By that time the people were half-drunk. They shouted, “Bring Samson out of the prison! Bring him here so that he can entertain us!” So they brought Samson from the prison and made fun of him. Then they made him stand in the center of the temple. They made him stand between the two pillars that held up the roof.
Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
26 Samson said to the servant who was leading him by his hand, “Place my hands against the two pillars. I want to rest against them.”
sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
27 At that time the temple was full of men and women. All the Philistine leaders were also there. And there were about 3,000 people on the roof, watching Samson and making fun of him.
To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
28 Then Samson prayed, saying, “Yahweh, my Lord, think about me again! Please give me strength one more time, so that I may get revenge on the Philistines for gouging out my eyes!”
Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
29 Then Samson put his hands on the two center pillars of the temple. He put his right hand on one pillar and his left hand on the other pillar.
Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
30 Then he shouted [to God], “Let me die with the Philistines!”, and he pushed with all his strength. [The pillars collapsed], and the temple crashed down on the Philistine leaders and all the other Philistine people, [and they all died]. So Samson killed more people when he died than he had killed all during his life.
Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
31 Later his brothers and their relatives went down [from Zorah to Gaza] to get his body. They took it back home and buried it between Zorah and Eshtaol, at the place where Samson’s father Manoah was buried. Samson had been Israel’s leader for 20 years.
Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.

< Judges 16 >