< Joel 1 >

1 [I am] Joel, the son of Pethuel. [This is] a message that Yahweh gave to me.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 You leaders [of Israel], and everyone else who lives in this country, listen [to this message]! Nothing [RHQ] like this has ever happened during the time that we have lived or the time when our ancestors lived.
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Tell your children about it, and tell your children to tell it to their children, and tell your grandchildren to tell it to their children.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 [I am talking about] the locusts that have eaten our crops. The first swarm of locusts came and cut [many of the leaves of the crops]; then another swarm came and ate [the rest of the leaves], then another swarm came hopping along, and finally another swarm came and they destroyed [everything else].
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 You people who are drunk, wake up! Wake up and wail loudly, because all the grapes are ruined, and so there will be no new wine [MTY]!
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 [Huge swarms of] locusts have entered our country. [They are like] [MET] a powerful army [that has very many soldiers], [with the result that] no one can count them. The locusts have teeth that are [as sharp as] the teeth of lions [DOU]!
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 They have destroyed our grapevines and our fig trees [by] stripping off [and eating all] the bark, with the result that the branches are white [and (bare/have no leaves on them)].
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Cry like [SIM] a young woman cries when the young man to whom she was (engaged/promised to marry) has died.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 There is no grain or wine for us to offer [as sacrifices] at the temple, [so] the priests who serve Yahweh are mourning/weeping.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 [The crops in] the fields have been ruined; [it is as though] [PRS] the ground is mourning. The grain has been destroyed, there are no [grapes to make] wine, and there is no [more olive] oil.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 You farmers, grieve! You who take care of grapevines, wail, because the grain has been destroyed; there is no wheat or barley growing.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 The grapevines and the fig trees have withered, and the pomegranate [trees] and palm [trees] and apricot [trees] have also dried up. The people are no longer joyful.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 You priests, put on [rough] sack clothes and wail. You who serve God [by offering sacrifices] on the altar, wear those rough sack clothes all night [to show that you are mourning], because there is no grain or wine to be offered at the temple of your God.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Tell the people that they should (fast/abstain from eating food). Tell the leaders and the other people to gather at the temple and to cry [out] to Yahweh [there].
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Terrible things are happening to us! It will soon be the time when Yahweh, [who is] the Almighty God, [will really punish us], [when he] will cause us to experience more disasters.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Our crops are already gone, and no [one is] rejoicing at all [DOU] at the temple of our God.
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 [When we plant] seeds, [they do not grow]; they dry up in the ground, so there are no crops to harvest. Our barns/storehouses are empty; there is no grain [to store in them].
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Our cattle groan, searching for a pasture with some grass to eat, and the sheep bleat because they are suffering.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 Yahweh, I cry [out] to you, because our pastures and our forests have dried up in the hot sunshine [MET].
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 [It is as though] even the wild animals cry [out] to you because all the streams have dried up. The rivers and streams are all dry, and the grass in the pastures is all parched.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joel 1 >