< Isaiah 39 >

1 Soon after that, Baladan’s son Merodach-Baladan, the King of Babylon, heard a report that Hezekiah had been very sick but that he had recovered. So he wrote some notes and gave them to some messengers to take to Hezekiah, along with a gift.
A wannan lokaci Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu da kuma kyauta, domin ya ji rashin lafiyarsa da kuma warkarwarsa.
2 [When the messengers arrived], Hezekiah welcomed them gladly. [Then] he showed them everything that was in his (treasure houses/places where very valuable things were kept)—the silver, the gold, the spices, and the nice-smelling [olive] oil. He also took them to see the place where they kept their soldiers’ weapons, and he showed them the other valuable things that were in the storehouses. Hezekiah showed them everything [LIT] that was in the palace or in other places [HYP].
Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
3 Then I went to King Hezekiah and asked him, “Where did those men come from, and what did they want?” He replied, “They came from the far away land of Babylon.”
Sai Ishaya annabi ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya kuma tambaye shi ya ce, “Mene ne waɗannan mutane suka faɗa, kuma daga ina suka fito?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Sun zo ne daga Babilon.”
4 I asked him, “What did they see in your palace?” Hezekiah replied, “They saw everything. I showed them absolutely everything that I own—all my valuable things.”
Annabi ya yi tambaya ya ce, “Mene ne suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga kome da kome a fadana. Babu abin da ban nuna musu a cikin ma’ajina ba.”
5 Then I said to Hezekiah, “Listen to this message from the Commander of the armies of angels:
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji maganar Ubangiji Maɗaukaki.
6 'There will be a time when everything in your palace, all the valuable things that your ancestors stored there up until the present time, will be carried away to Babylon. Yahweh says that there will be nothing left.
Tabbatacce lokaci yana zuwa sa’ad da kome da yake cikin fadanka, da kuma dukan abin da kakanninka suka ajiye har yă zuwa yau, za a kwashe zuwa Babilon babu abin da za a bari, in ji Ubangiji.
7 Furthermore, some of your sons will be forced to go to Babylon. They will be castrated in order that they can become servants in the palace of the king of Babylon.'”
Waɗansu cikin zuriyarka, nama da jininka waɗanda za a haifa maka, za a kwashe su a tafi, za su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
8 Then Hezekiah replied to me, “That message from Yahweh that you have given to me is good.” He said that because he was thinking, “Even if that happens, there will be peace, and people in this country will be safe during the time that I am alive.”
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka yi tana da kyau.” Gama ya yi tunani a ransa cewa, “Salama da kāriya za su kasance a zamanina.”

< Isaiah 39 >