< Hosea 6 >

1 [The Israeli people say, ] “Come, let’s return to Yahweh! He has caused [us] to be injured, but he will heal us. He has caused [us] to be wounded, but [it is as though] he will put bandages on our wounds [MET].
“Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
2 After a very short time he will revive us; in less than three days he will restore us in order that we may live in his presence.
Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
3 We must try to know Yahweh; [if we do that, ] he will come [and help] us, as surely as the sun rises [every morning], as surely as rain falls every winter/cold season, and as surely as the rain falls again (in the springtime/at the end of the cold season).”
Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
4 [But Yahweh knows they are insincere; ] [so he says to them, ] “You [people of] Israel, and you [people of] Judah, [I do not know] [RHQ] what I should do to you. Your being faithful [to me will disappear as quickly] as [SIM] the morning mist [disappears], like [SIM] the dew [on the ground] that disappears quickly [when the sun shines].
“Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
5 I warned [HYP] you by [the messages that I gave to] the prophets, [but you did not pay attention to my messages]. Therefore I will completely destroy you; the punishment that I give you will strike you like lightning.
Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
6 I want [my people] to faithfully love [me] more than [I want them to offer] sacrifices [to me]; [I want them] to know me more than [I want them to] completely burn sacrifices [on the altar].
Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
7 But they have refused to obey my agreement, [just] like Adam did; they have not been faithful to me.
Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
8 Gilead is a city [full] of people who do wicked things; [in the streets] are the bloody footprints [of those who have murdered others].
Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
9 The priests are like [SIM] bandits who wait (in ambushes/along the road) to attack people; they murder [people who are walking] on the road to Shechem, and they commit other disgraceful crimes.
Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
10 I have seen horrible things [being done] in Israel [MTY]. The people have abandoned me [like prostitutes who have abandoned their husbands] [MET]; [so the people of] Israel have become unacceptable to me.
Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
11 And you [people of] Judah, I have appointed a time when I will punish [MET] you, too. Whenever I wanted to enable my people to prosper again,”
“Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,

< Hosea 6 >