< Ezekiel 43 >

1 Then [in the vision] the man brought me to the entrance on the east side.
Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
2 Suddenly I saw the glory/brightness of the God of Israel coming from the east. The sound of his coming was like the roar of a rushing river, and all that area shone with his glory.
sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
3 What I saw in this vision was like what I saw in the visions that I had seen [previously, first] by the Kebar River and [later] when God came to destroy Jerusalem. I prostrated myself on the ground.
Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
4 The glory of Yahweh entered the temple through the east entrance.
Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
5 Then the Spirit lifted me up and brought me into the inner courtyard, and the glory of Yahweh filled the temple.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
6 [Then] while the man was standing beside me, I heard someone speak to me from inside the temple.
Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
7 He said, “You human, this is [my temple], the place [I sit on] my throne and where I rest my feet. This is where I will live with the Israeli people forever. The Israeli people and their kings will never again disgrace me [SYN] by worshiping other gods [MET] at the shrines on their hilltops, or by [building] monuments to honor their kings who have died.
Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
8 They placed their altars near mine, and the doorposts of their [temples] were next to the doorposts of my [temple]. There was only a wall between them. And they disgraced me by the detestable things that they did. So, being very angry with them, I got rid of them.
Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
9 Now they must stop this disgusting worship of idols and these rituals to honor their kings who have died. If they stop doing those things, I will live among them forever.
Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
10 You human, describe to the Israeli people what this temple that I have shown you [in a vision] is like, in order that they will be ashamed of the sins that they have committed [which resulted in their temple in Jerusalem being destroyed].
“Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
11 If they are ashamed of all [the evil things] that they have done, tell them [all] about the temple [that I showed you]: its design/shape, the exits and entrances, [and everything else about it]. And tell them all my laws and regulations about worshiping me there. Write all these things down while they watch you, in order that they will be able to faithfully obey those laws.
kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
12 And this is the supreme law about the temple [DOU]: All of the area on top of the hill [where the temple will be built] must be kept sacred and holy.”
“Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
13 These are the measurements of the altar, using the same kind of measuring stick that was used for the temple area: There is a gutter around the altar that is (21 in./53 cm.) deep and (21 in./53 cm.) wide. There is a rim around it that is (9 in./23 cm.) wide.
“Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
14 The lower part of the gutter is (3-1/2 feet/1.1 meters) high to the lower ledge/rim that surrounds the altar. The lower ledge is (21 in./53 cm.) wide. The upper part of the altar is (7 feet/2.1 meters) high, up to the upper ledge. That ledge is also (21 in./53 cm.) wide.
Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
15 The (hearth/place where the sacrifices are burned) at the top of the altar is another (7 feet/2.2 meters) high, and there is a projection that juts/extends up from each of the four corners.
Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
16 That place at the top of the altar is square, (21 feet/6.4 meters) on each side.
Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
17 The upper ledge is also a square, (24-1/2 feet/7.4 meters) on each side. There is a (21 in./53 cm.) gutter [at the bottom of the altar], and a (10.5 in./26.6 cm.) rim all around it. There are steps up to the east side of the altar.”
Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
18 Then the man said to me, “You human, this is what Yahweh the Lord says: These are the regulations for sacrificing offerings that will be completely burned and for sprinkling the blood against the sides of the altar when it is built:
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
19 You must present to the priests a young bull to be an offering to cause the altar to be acceptable to me. The priests are descendants of Levi, from the clan of Zadok, who come near to the altar to serve me.
Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 You must take some of the blood [from the bull that is sacrificed], and smear it on the four projections of the altar and on the four corners of the upper ledge, and all around the rim, to cause the altar to be acceptable to me, and to consecrate it.
Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
21 You must burn that bull outside the temple in the part of the temple area [that I have] designated for that.
Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
22 The next day, you must offer a male goat that has no defects, to be an offering to cause the altar to be acceptable to me. Then you must purify the altar again, like you did with the bull that was sacrificed.
“A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
23 When you have finished doing all that, you must offer a young bull and a ram, both of them without any defects.
Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
24 You must offer them to [me], Yahweh, and the priests must sprinkle salt on them and completely burn them [on the altar] for a sacrifice to me.
Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
25 [Then], each day for seven days, you must bring [to the priest] a male goat [to be sacrificed] for an offering to cause the altar to be acceptable to me. You must also sacrifice a young bull and a ram, [each] without any defect.
“Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
26 For seven days the priests will consecrate the altar and cause it to be acceptable to me. By doing that they will dedicate it to me.
Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
27 At the end of those seven days, starting on the following day, the priests will continue to put on the altar offerings to be completely burned and offerings to maintain fellowship with me. Then I will accept you. [That it what I], Yahweh the Lord, declare.”
A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 43 >