< Ezekiel 33 >

1 Yahweh gave me another message. He said,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “You human, speak to your fellow Israelis and say this to them: ‘When I bring an enemy army [MTY] to attack a country, and the people of that country choose one of their men and appoint him to be a watchman,
“Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
3 if he sees the enemy army [MTY] coming to attack his country, and he blows a trumpet to warn the people,
ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
4 if anyone hears the trumpet and does not heed the warning, and as a result he is killed by the sword [of one of his enemies], he will be responsible for his own death [MTY].
in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
5 If he had heeded the warning, he would have (have saved his life/still be alive). But because he heard the sound of the trumpet and did not heed that warning, his death will be his own fault.
Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
6 But if the watchman sees the enemy army [MTY] coming and does not blow the trumpet to warn the people, and one of his people is killed by an enemy sword, that person will die because of his sin, but I will consider that the watchman is responsible for that man’s death.’
Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
7 So, you human, I have appointed you to be a watchman for the Israeli people [MTY]. So always listen to what I say and warn the people for me.
“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
8 When I say to some wicked person, ‘You wicked person, you will surely die [because of your sins,’ you must tell him that]. If you do not speak to that person to warn him that he should turn away from his sins, that wicked person will die because of his sins, but I will say that you are responsible for his death [MTY].
Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
9 But if you warn that wicked person that he should turn away from his sins, and he does not do that, he will die because of his sins, but you will have saved your life.
Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
10 You human, say to the Israeli people, ‘This is what you all are saying: “[The guilt that we have for] disobeying God’s laws and sinning is like a heavy weight on us, and it is hurting us, and we are slowly dying. So what can we do to continue to remain alive?”’
“Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
11 Say to them, ‘Yahweh the Lord says, “As surely as I am alive, I am not happy when wicked people die; I would prefer that they turn away from their wicked behavior and continue to live. So repent! Turn away from your evil behavior! You Israeli people, do you really want to die [RHQ]?”’
Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
12 Therefore, you human, say to your fellow Israelis, ‘If righteous people start to disobey me, their being righteous previously will not save them [from being punished]. And if wicked people turn away from their wicked behavior, they will not die because of the sins that they committed [previously]. And if righteous people start to sin, they will not be allowed to remain alive because of their formerly being righteous.’
“Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
13 If I tell righteous people that they will surely remain alive, but then they trust/think that because they have been righteous previously, they can start to do evil [and not be punished], I will not think about the righteous things that they did previously; they will die because of the evil things that they are doing.
In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
14 And if I say to some wicked person, ‘You will surely die [because of your sins],’ that person may turn away from his sinful behavior and do what is just and right [DOU].
Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
15 For example, he may return what he took from another person to guarantee [that that person would pay back what he owes], or he may return things that he has stolen, and he may obey the laws that will enable [those who obey them] to remain alive, and he will not continue to do evil things. If that happens, he will surely remain alive; he will not die [because of the sins that he committed previously].
in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
16 I will not think about the sins that he has committed; he will surely remain alive.
Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
17 Your fellow Israelis say, ‘What Yahweh does is not fair.’ But it is your behavior that is not fair.
“Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
18 If a righteous person turns away from doing what is righteous and starts to do what is evil, [it is fair that] he die because of his sins.
In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
19 And if a wicked person turns away from his wicked behavior and does what is right and fair [DOU], [it is fair] for him to remain alive because of doing that.
Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
20 But you Israeli people still say, ‘What Yahweh does is not fair.’ But I will judge each of you for what you do.”
Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
21 Almost twelve years [after we had been taken to Babylonia], on the fifth day of the tenth month [of that year], a man who had escaped from Jerusalem came to me [in Babylon] and said, “Jerusalem has been captured!”
A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
22 The evening before that man arrived, Yahweh took control [MTY] of me, and when that man arrived, Yahweh enabled me to speak again; I was no longer forced to be silent.
To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
23 Then Yahweh gave a message to me. He said,
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
24 “You human, the people who are living in the ruins in Israel are saying, ‘Abraham was only one person, but Yahweh [promised him that he and his descendants] would possess this land. But we are many; so surely this land has been given to us [by Yahweh] to continue to possess.’
“Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
25 So send a message to them. Say, ‘This is what Yahweh the Lord says: You eat meat that still has the animal’s blood in it. You still worship idols. And you still murder others [MTY]. So, (should this land belong to you?/this land should certainly not belong to you!) [RHQ]
Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
26 You rely on using your swords [to obtain things that you want]. You do many detestable things. Each of you has sex with other men’s wives. So (why should you continue to possess the land of Israel?/you should not continue to possess this land!) [RHQ]’
Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
27 Send this message to them: ‘This is what Yahweh the Lord says: As surely as I am alive, those who are left in the ruins [in Jerusalem] will also be killed by [their enemies’] swords, and those who are living in the countryside will be killed by wild animals, and those who are living in forts and caves will die from a plague.
“Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
28 I will cause your country to become a desolate wasteland. You will no longer be proud of being a strong country. The mountains of Israel will become very desolate, with the result that no one will walk across them.
Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
29 Then, when I have caused your country to become a desolate wasteland because of all the detestable things that you have done, you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].’
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
30 As for you, you human, your fellow Israelis [here in Babylon] are talking about you along the city walls and at the doors of their houses. They are saying to each other, ‘Come and listen to the message that has come from Yahweh!’
“Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
31 My people come to you as they often have done, and they sit in front of you to listen to what you say. But they do not do what you tell them that they must do. With their mouths they say that they love me, but in their inner beings they are eager to acquire things by doing what is unjust.
Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
32 To them, you are only a man who sings love songs with a beautiful voice, and you play a musical instrument well. They hear what you say, but they do not do what you tell them to do.
Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
33 The terrible things that I have said will happen to them will surely happen. And then they will know that a prophet has been among them, [and that you are that prophet].”
“Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”

< Ezekiel 33 >