< Ezekiel 19 >

1 [Yahweh said to me, “Ezekiel], sing a sad funeral [a which will be a parable] [two of the] kings of Israel.
“Ka yi makoki game da sarakunan Isra’ila
2 Say [to the Israeli people], ‘[It is as though] [MET] your mother was a brave female lion who raised her cubs among [other] lions.
ka ce, “‘Mahaifiyarki zakanya ce cikin zakoki! Takan kwanta cikin’yan zakoki ta kuma yi renon kwiyakwiyanta.
3 She taught one of them to [for other animals to kill], and he [even] learned [kill and] eat people.
Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta, ya yi girma ya zama zaki mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
4 [When people from other] nations heard about him, they trapped him in a pit. Then they used hooks to drag him to Egypt.
Al’ummai suka ji labarinsa, aka kuma kama shi cikin raminsu. Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa ƙasar Masar.
5 His mother waited for him [to return], but [soon] she stopped hoping/expecting [that he would return]. So she raised another cub who [also] became very fierce.
“‘Sa’ad da ta ga sa zuciyarta bai cika ba, abin da take fata gani ya tafi, sai ta ɗauki wani daga cikin kwiyakwiyanta ta mai da shi zaki mai ƙarfi.
6 He hunted along with [other] [for animals to kill], and he even learned [kill and] eat people.
Ya yi ta yawo a cikin zakoki, gama yanzu shi zaki ne mai ƙarfi. Ya koyi yayyage abin da ya yi farauta yakan kuma cinye mutane.
7 He destroyed forts, and he ruined cities. When he roared [loudly], everyone was terrified.
Ya rurrushe kagaransu ya kuma ragargaza biranensu. Ƙasar da dukan waɗanda suke cikinta sun tsorata da jin rurinsa.
8 So [people of other] nations planned to kill him, and men came from many places to spread out a net for him, and they caught him in a trap.
Sai al’ummai suka tayar masa, waɗannan daga yankunan da suke kewaye. Suka yafa raga dominsa ya kuwa fāɗa cikin raminsu.
9 They tied him with chains and took him to Babylonia. And [there] he was locked in a prison, with the result that [no one on] the hills of Israel ever heard him roar again.’ [Also, say to the Israeli people, ]
Da ƙugiyoyi suka ja shi cikin keji suka kawo shi wurin sarkin Babilon. Suka sa shi cikin kurkuku, saboda haka ba a ƙara jin rurinsa a kan duwatsun Isra’ila ba.
10 ‘[It is as though] [SIM] your mother was a grapevine that was planted along a stream. There was plenty of water, so it had lots of branches and produced [a lot of] grapes.
“‘Mahaifiyarku kamar kuringa ce a cikin gonar inabi da aka shuka kusa da ruwa; ta ba da’ya’ya da kuma cikakkun rassa saboda yalwan ruwa.
11 That grapevine grew and became taller than all the nearby trees; [everyone could] see that it was very strong and healthy. And those branches were good for making scepters that symbolize the power/ [of a king].
Rassanta suka yi ƙarfi, suka dace da sandar mai mulki. Ta yi tsayi zuwa sama ana ganin ta saboda tsayinta da kuma saboda yawan rassanta.
12 [Yahweh] became very angry, so he pulled up the vine by its roots and threw it on the ground, where the [very hot] winds from the desert dried up all its fruit. The strong branches wilted and were burned in a fire.
Amma aka tumɓuke ta cikin fushi aka jefar da ita a ƙasa. Iskar gabas ta sa ta yanƙwane, aka kakkaɓe’ya’yanta; rassanta masu ƙarfi suka bushe wuta kuma ta cinye su.
13 Now that vine has been planted in a hot, dry desert.
Yanzu an shuka ta a hamada, a busasshiyar ƙasa marar ruwa.
14 A fire started to burn its stem, and then started to burn the branches and burned all the grapes. [Now] not [even] one strong branch remains; they will never become scepters for a king.’ That funeral song must be sung very sadly.”
Wuta ta fito daga jikin rassanta ta cinye’ya’yanta. Babu sauran reshe mai ƙarfin da ya rage a kanta da ya dace da sandar mai mulki.’ Wannan waƙa ce kuma za a yi amfani da ita a matsayin makoki.”

< Ezekiel 19 >