< Exodus 16 >

1 They/We left Elim, and all the Israeli people came to the desert [named] Sin. That is between Elim and Sinai [Mountain]. That was on the fifteenth day of the second month after they/we left Egypt.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 There in the desert, the Israeli [HYP] people complained to Aaron and Moses/me.
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 They said to them/us, “We wish that Yahweh had killed us in Egypt! There we had meat to eat, and all the bread that we wanted. But you have brought us into this desert in order that we will all starve to death!”
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 Yahweh said to Moses/me, “Listen to what I am going [to do]. I am going to send something from the sky that will [take the place of] bread for all of you. When I do that, the people must go out of their tents every day and gather just enough to eat on that day. [When I do that], I will find out whether they will obey my instructions or not.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 On the sixth day [after I start doing that], they will be able to gather twice as much as on the other days, [and not have to gather any on the seventh day]. Then they can prepare it [to eat it on the 6th and 7th days].”
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 So Aaron and Moses/I said to all the Israeli people, “This evening you will know that it was Yahweh, [not we], who brought you out of Egypt.
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 And tomorrow morning you will see how great Yahweh is, because he has heard what you have complained about. He is the one whom you have really complained to, because we are just his servants.” [RHQ]
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 Then Moses/I also said, “[From now on, each] evening Yahweh will give you meat to eat, and [each] morning he will give you [something that will take the place of] bread, because he has heard what you have complained about. Yahweh is the one to whom you have really complained, not us. We are just his servants.” [RHQ]
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 Then Moses/I said to Aaron, “Tell all the Israeli people, ‘Come and stand here in the presence of Yahweh, because he has heard what you have been complaining about.’”
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 So Aaron told them that. And as Aaron was talking to all the Israeli people, they looked toward the desert, and were surprised to see the (dazzling light/incredible brightness) of Yahweh in the cloud [that had been leading them].
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 Then Yahweh said to Moses/me,
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 “I have heard what the Israeli people have been complaining about. So say to them, ‘From now on, each evening, you will have meat to eat. And each morning you will have something that will take the place of bread. You will have all you want of it to eat.’ Then you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].”
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 That evening, (quails/small plump birds) appeared, and [there were so many that] they covered the campsite. The next morning there was [something like] dew all around the campsite.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 When the dew evaporated, on the surface of the desert there was a thick layer of something that looked like white flakes. It looked like frost.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 When the Israeli people saw it, since they [had never seen it before and] did not know what it was, they said to each other, “What is it?” Moses/I replied to them, “It is something Yahweh has given you to eat, to take the place of bread.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 This is what Yahweh has commanded: ‘Each of you should gather as much as you need to eat. Gather two quarts/liters for each person who lives in your tents.’”
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 So that is what the Israeli people did. Some gathered more and some gathered less.
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 But when they measured [what they had gathered], those that had gathered a lot did not have anything left over. And those that gathered less still had enough to eat. Each person gathered just what they needed.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 Moses/I said to them, “Do not leave any of it to eat tomorrow morning!”
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 But some of them did not pay any attention to what Moses/I said. They kept some of it until the next morning. But it was full of maggots and smelled rotten. And that made Moses/me angry.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 Each morning they gathered as much as they needed. But [later], when the sun got hot, [what was left on the ground] melted.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 On the sixth day after they started gathering it, each person was able to gather four quarts/liters, which was twice [as much as they gathered on the other days]. When the leaders of the people came to Moses/me and told him/me [about that],
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 Moses/I said to them, “This is what Yahweh has commanded: ‘Tomorrow will be a day for you to rest completely. It will be a day dedicated to Yahweh. So today, bake or boil what you will [need for today and for tomorrow]. Whatever is left [this evening], you should put aside and keep it [to eat] tomorrow.’”
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 So they did what Moses/I commanded. What was left over, they kept until the next day. It did not spoil and did not get maggots in it!
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 [On that day], Moses/I said, “Eat today [what you have saved from yesterday], because today is a day dedicated to Yahweh. Today you will not find any of that food outside.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 [Every week], you must gather it for six days; but on the seventh day, which will be a day of rest, you will not find any.”
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 On the seventh day, some of the people went outside their tents to gather some of that food, but there was none.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 Then Yahweh [told Moses/me to say this to] the people: “How long will you people refuse to do all the things that I tell you?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 Listen! Yahweh has given you a day of rest. So on the sixth day [of each week], he will be giving you enough of this food for two days. Each of you should stay in his tent [and do no work] on the seventh day!”
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 So the people rested on the seventh day.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 The Israeli people called this food manna, [which sounds like the words in their language that mean ‘what is it]?’ It looked like small seeds [called] coriander, but it was white, and it tasted like thin wafers/biscuits made with honey.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 Moses/I said, “This is what Yahweh has commanded: ‘You must keep two quarts/liters of it for all future generations, so that they can see the [food that took the place of] bread that I gave to your [ancestors] when I brought them out of Egypt.’”
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 And he/I said to Aaron, “Take a jar, and put two quarts of manna in it. Then put it [in a place] where Yahweh can see it. It is to be kept like that for all future generations.”
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 [Many years later], as Yahweh had commanded Moses/me, Aaron put the jar in front of the box [that contained the stone slabs on which] the Ten Commandments [were written].
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 The Israeli people were able to eat manna [every day] for 40 years, until they came to the border of Canaan land.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 (The standard measure [that they used at that time] held 20 quarts/liters.)
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exodus 16 >