< Esther 6 >

1 That night the king was unable to sleep, so he [summoned] a servant [and] told [him] to bring the records of what had happened during all the time he had been king. [So the servant brought the records] and read some of them to the king.
A daren nan, sarki bai iya barci ba, saboda haka ya ba da umarni a kawo, a kuma karanta masa littafin tarihi na shekara-shekara, da rubutaccen labarin mulkinsa.
2 [The servant read about] Bigthana and Teresh, the two men who had guarded the entrance to the king’s rooms. He read the account of when Mordecai had found out that they planned to assassinate the king [and that he had told the king about it].
Aka tarar, a rubuce a ciki, cewa Mordekai ya tone ƙulle-ƙullen Bigtana da Teresh, biyu daga hafsoshin sarki, waɗanda suke tsaron mashigin ƙofa, waɗanda suka ƙulla su kashe Sarki Zerzes.
3 The king asked [some of his servants], “What did we do to reward Mordecai or show that we appreciate what he did?” The servants replied, “We did not do anything for him.”
Sarki ya ce, “Wace girma da daraja ce aka ba wa Mordekai saboda wannan?” Masu hidimarsa suka ce, “Ba a yi masa wani abu ba.”
4 At that moment, Haman entered the outer courtyard of the palace. He wanted to talk to the king about hanging Mordecai on the gallows that he had [just] set up. The king [saw him and] said, “Who is [that out there] in the courtyard?”
Sarki ya ce, “Wa yake a haraba?” Daidai lokacin kuwa Haman ya shigo harabar waje na fada don yă yi magana da sarki a kan a rataye Mordekai a wurin rataye mai laifin da ya shirya.
5 His servants replied, “That is Haman standing there in the courtyard.” The king said, “Bring him in [here]!”
Masu yi wa sarki hidima, suka amsa, “Haman yana tsaye a haraba.” Sarki ya umarta, “A kawo shi ciki.”
6 When Haman came in, the king asked him, “What should I do for a man whom I want to honor?” Haman thought to himself, “(Whom would the king like to honor more than me?/I think there is no one whom the king would like to honor more than me!)” [RHQ]
Sa’an nan Haman ya shigo, sai sarki ya ce masa, “Me ya kamata a yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama?” Haman dai ya yi tunani a ransa ya ce, “Wane ne sarki zai girmama in ba ni ba?”
7 So he replied to the king, “If there is someone you wish to honor,
Sai ya amsa wa sarki cewa, “Saboda mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama,
8 you should [tell your servants to] bring him one of the robes you wear [you to show that you are] the king. Also tell them to bring one of the horses you have ridden. Tell them to put a fancy headdress on the horse’s head to show that it belongs to you, the king.
bari a kawo rigar sarautar da sarki ya taɓa sawa, da kuma dokin da sarki ya taɓa hawa, wanda aka sa kambin sarauta a kai.
9 Then tell one of your very important officials to put the robe on the man whom you want to honor, and tell that man to sit on the horse, and then lead the horse through the city streets. And tell that official to keep shouting, ‘This is what (the king does/is doing) for the man whom he wants to honor!’”
Sa’an nan, bari a ba da rigar da kuma dokin wa ɗaya daga cikin manyan sarakuna mafi kirki na sarki. Bari shi kuma yă sa wannan riga wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama, a kuma bi da shi a bisan doki ko’ina a titunan birni, ana shela a gabansa ana cewa, ‘Wannan shi ne abin da ake yin wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!’”
10 The king replied to Haman, “[Fine]! Go and do what you said immediately! Get my robe and my horse, and do just what you suggested! Do it for Mordecai, the Jew, who is sitting [outside] at the gate of the palace. Do not forget anything that you suggested!”
Sarki ya umarci Haman ya ce, “Tafi yanzu ka karɓi rigar da dokin, ka kuma yi yadda ka shawarta wa Mordekai, mutumin Yahudan nan, wanda yake zama a bakin ƙofar sarki. Kada ka kāsa yin kome daga cikin abin da ka faɗa.”
11 So Haman did what the king said. He got the robe and the horse. He put the robe on Mordecai, and as Mordecai sat on the horse, Haman led the horse through the city streets proclaiming “This is what the king (does/is doing) for the man whom the king wants to honor!”
Saboda haka, Haman ya karɓo rigar da dokin. Ya sa wa Mordekai rigar, ya kuma bi da shi a kan doki ko’ina a titunan birnin, yana shela a gabansa yana cewa, “Wannan shi ne abin da ake yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!”
12 Then, Mordecai returned [and sat] at the gate of the palace. But Haman hurried home, covering his face [because he felt] completely disgraced/humiliated.
Daga baya, Mordekai ya dawo zuwa ƙofar sarki. Amma Haman ya ruga gida, kansa a rufe, saboda baƙin ciki.
13 He told his wife Zeresh and his friends everything that had happened to him that day. Then his wife and his friends said to him, “Mordecai, the man who has caused you to be completely disgraced/humiliated, is a Jew. [It is clear that the God whom the Jews worship is fighting for them.] So you will never be able to defeat Mordecai. He will defeat you!”
Ya je ya faɗa wa matarsa Zeresh, da dukan abokansa, me ya same shi. Masu ba shi shawara, da matarsa Zeresh, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara fāɗuwa a gabansa, daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, tabbatacce za ka fāɗi a gabansa!”
14 And while they were still talking, some of the king’s officials arrived to take Haman quickly to the banquet/feast that Esther had prepared.
Suna cikin magana da shi ke nan, sai ga bābānnin sarki, suka iso suka kuma hanzarta da Haman zuwa liyafar da Esta ta shirya.

< Esther 6 >