< Deuteronomy 14 >

1 “We are people who belong to Yahweh our God. So, when people die, do not show that you are grieving by gashing/cutting yourselves or by shaving the hair on your foreheads [like the other people-groups do].
Ku’ya’yan Ubangiji Allahnku ne. Kada ku yi wa kanku zāne, ko ku yi wa kanku aski irin da akan bar sanƙo, saboda wanda ya mutu,
2 We belong to Yahweh alone. Yahweh chose us from all the other people-groups on the earth to be his special people.
gama ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Daga dukan mutane a fuskar duniya, Ubangiji ya zaɓe ku, ku zama abin mallakarsa.
3 “Do not eat anything that [Yahweh] detests.
Kada ku ci wani haramtaccen abu.
4 The animals [whose meat] you are permitted to eat are cattle, sheep, goats,
Waɗannan su ne dabbobin da za ku iya ci, saniya, tunkiya, akuya,
5 deer, gazelles, wild goats, antelopes, and mountain sheep.
mariri, barewa, mariya, makwarna, mazo, gada da kuma tunkiyar dutse.
6 Those are animals that have split hoofs and that also (chew their cuds/regurgitate their food [from their stomachs] to chew it again).
Za ku iya cin duk dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take sāke tona abin da suka riga suka haɗiye.
7 But there are other animals that chew their cuds that you must not eat. Those are camels, rabbits, and rock badgers. They chew their cuds, but their hooves are not split. So they are not acceptable for you to eat.
Amma, cikin waɗanda suke sāke tona abin da suka riga suka haɗiye ɗin, ko suke da rababben kofato, ba za ku ci raƙumi, zomo ko rema ba. Ko da yake suna sāke tona abin da suka riga suka haɗiye, suna kuma da rababben kofato, su ɗin marar tsarki ne gare ku.
8 Do not eat pigs. They are unacceptable for you to eat; their hooves are split, but they do not chew cud. Do not eat the meat of those animals; do not even touch their dead bodies.
Alade ma marar tsarki ne; ko da yake yana da rababben kofato, shi ba ya sāke tona abin da ya riga ya haɗiye. Ba za ku ci namansu ko ku taɓa gawarsu ba.
9 You are permitted to eat any fish that has scales and fins.
Cikin dukan halittun da suke cikin ruwa, za ku iya cin duk wani da yake da ƙege da ɓamɓaroki.
10 But anything else [that lives in the water] that does not have scales and fins, you must not eat, because [if you eat them], you will become unacceptable [to Yahweh].
Amma duk wani abin da ba shi da ƙege da ɓamɓaroki, ba za ku ci ba; gama marar tsarki ne gare ku.
11 “You are permitted to eat the flesh of any bird that is acceptable [to Yahweh].
Za ku iya cin kowane tsuntsu mai tsabta.
12 But eagles, vultures, black vultures,
Amma waɗannan ba za ku ci ba, gaggafa, ungulu, ungulun kwakwa,
13 buzzards, all kinds of kites,
duki, buga zaɓi, kowace irin shirwa,
14 all kinds of crows,
kowane irin hankaka,
15 ostriches, seagulls,
jimina, ƙururu, bubuƙuwa, kowane irin shaho,
16 owls, hawks, falcons,
da mujiya, da babbar mujiya, ɗuskwi,
17 pelicans, vultures that eat dead animals, cormorants,
kwasakwasa, ungulu, da babba da jaka,
18 storks, herons, hoopoes, and bats, you must not eat.
zalɓe, kowane irin jinjimi, katutu, da kuma jamage.
19 “All insects with wings [and which walk on the ground] are unacceptable [to Yahweh]; do not eat them.
Dukan’yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe, haram ne a gare ku, kada ku ci su.
20 But other insects with wings [and which hop along the ground] are acceptable to eat.
Amma duk wata halitta mai fikafikai mai tsabta ce, za ku iya ci.
21 “Do not eat any animal that has died naturally, [because its blood has not been drained out]. You may allow foreigners who live among you to eat those things or you may sell them to other foreigners. But you belong to Yahweh our God; [and those who belong to him are not permitted to eat the meat of animals whose blood has not been drained out]. “You must not cook a young sheep or goat in its mother’s milk.”
Kada ku ci abin da kun samu ya riga ya mutu. Za ku iya ba wa baren da yake zama a cikin wani daga biranenku, zai kuwa iya cinsa, ko kuwa za ku iya sayar da shi wa baƙo. Amma ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madara mamansa.
22 “Once each year you must set apart (a tithe/10 percent) of all the crops that are produced/harvested in your fields.
Ku tabbata kun keɓe kashi ɗaya bisa goma na amfanin gonakinku kowace shekara.
23 Take those things to the place that Yahweh our God will choose [for you to worship him]. There eat the tithes of your grain, your wine, your [olive] oil, and the meat of the firstborn male animals of your cattle and your sheep. Do this in order that you may learn to always revere Yahweh, [the one who has blessed you by giving you these things].
Ku ci zakkar hatsinku, da na sabon ruwan inabinku, da na manku, da kuma na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, don ku koyi girmama Ubangiji Allahnku kullum.
24 If the place that Yahweh has chosen [for you to worship him] is very far from your home, with the result that you are not able to take there the tithes [of your crops] with which Yahweh has blessed you, do this:
Amma in wurin nan yana da nisa sosai, Ubangiji Allahnku kuma ya albarkace ku, ba za ku kuwa iya riƙe zakkarku ba (Saboda wurin da Ubangiji ya zaɓa yă sa Sunansa ya yi nisa sosai),
25 Sell [IDM] the tithes of your crops, wrap the money carefully [in a cloth], and take it with you to the place of worship that Yahweh has chosen.
to, sai ku sayar da zakkar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa.
26 There, [with that money], you may buy whatever you want to—beef or lamb or wine or fermented drinks. And there, in the presence of Yahweh, you and your families should eat [and drink] those things and be happy.
Yi amfani da kuɗin ku saya duk abin da kuke so, ko shanu, ko tumaki, ko ruwan inabi, ko dai wani abin shan da ya yi tsami, ko kuwa duk abin da kuke so. Sai ku da gidanku, ku ci a can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku kuma yi farin ciki.
27 But be sure to not neglect/forget [to help] the descendants of Levi who live in your towns, because they will not own any land.
Kada dai ku manta da Lawiyawan da suke zama a biranenku, gama ba su da rabo, ko gādo na kansu.
28 “At the end of every three years, bring a tithe of all your crops that have been produced/harvested in that year and store it in your towns.
A ƙarshen kowace shekara uku, ku kawo dukan zakkarku na amfanin gona na wannan shekara, ku ajiye su a cikin birane,
29 That food is for the descendants of Levi, because they do not have their own land, and for foreigners [who live among you], and for orphans and widows who live in your towns. They are permitted to come [to where the food is stored] and take what they need. Do that in order that Yahweh our God will bless you in everything that you do.”
saboda Lawiyawa (waɗanda ba su da rabo ko gādo na kansu) da baƙo, da marayu, da kuma gwauraye, waɗanda suke zama a biranenku, su zo su ci su ƙoshi, ta haka Ubangiji Allahnku zai albarkace ku cikin dukan ayyukan hannuwanku.

< Deuteronomy 14 >