< Acts 20 >

1 After the people at Ephesus had stopped rioting, Paul summoned the believers. He encouraged them [to continue to trust in the Lord Jesus. Soon] after that, he told them goodbye and left to go to Macedonia [province].
Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
2 [After he arrived] there, he visited [each town where there were believers], and encouraged them. Then he arrived in Greece [province], [which is also called Achaia].
Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
3 He stayed there for three months. Then he planned to return to Syria by ship, but [he heard that] some of the Jews [SYN] [in that area] were planning to kill him [as he traveled. So] he decided instead to go [by land, and he traveled] again through Macedonia.
inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
4 The men who were going to travel with him [to Jerusalem were] Sopater, [who was] a son of Pyrrhus, who grew up in Berea [town]; Aristarchus and Secundus, who were from Thessalonica [city; ] Gaius, [who was] from Derbe [town; ] Timothy, [who was from Galatia province; ] and Tychicus and Trophimus who were from Asia [province].
Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
5 Those [seven] men went ahead of [Paul and me, Luke, by ship from Macedonia, so] they got to Troas [before we did and] waited for [the two of] us there.
Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
6 [But we two(exc) traveled by land as far as] Philippi [city]. After the Jewish festival [when they eat] unleavened bread, we got on a ship [that was going from] the port near [Philippi to Troas city]. After five days we [(exc)] arrived at Troas and we met the other men who had traveled there [ahead of us]. Then we [all] stayed in Troas for seven days.
Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
7 (On Sunday evening/On the evening of the first day of the week), we [(exc) and the other believers there] gathered together to celebrate the Lord’s Supper [and to eat other food] [SYN]. Paul spoke to the believers. He continued teaching them until midnight, because he was planning to leave [Troas] the next day.
A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
8 Many [oil] lamps were burning in the upstairs room in which we [(exc)] had gathered, [so the fumes caused some people to become sleepy].
Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
9 A young man whose name was Eutychus was there. He was seated on [the sill of] an [open] window [on the third story of the house]. As Paul continued talking for a long time, Eutychus became sleepier and sleepier. Finally, he was sound/really asleep. He fell [out of the window] from the third story down [to the ground. Some of the believers went down] immediately and picked him up. [But he was] dead.
Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
10 Paul [also] went down. He lay down and stretched out on top of the young man and put his arms around him. Then he said [to the people who were standing around], “Do not worry, he is alive [again now]!”
Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
11 Then Paul, [along with the others], went upstairs again and they ate the Lord’s Supper and other food [SYN]. Afterwards, Paul conversed with the believers until dawn. Then he left.
Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
12 The [other] people took the young man [home], and were greatly encouraged because he was alive [again].
Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
13 We then went to the ship. Paul did not get on the ship [with us in Troas], because he preferred to go [more quickly] overland to Assos [town]. The rest of us got on the ship and sailed for Assos.
Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
14 We [(exc)] met Paul in Assos. He got on [the ship] with us, and we sailed to Mitylene [town].
Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
15 The day after [we reached Mitylene], we [sailed from there and] arrived [at a place] near Kios [Island]. The day after that, we sailed to Samos [Island]. The next day we [left Samos and] sailed to Miletus [town].
Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
16 [Miletus was just south of Ephesus city]. Paul had [earlier] decided that he would not get on a ship that would stop at Ephesus, because he did not want to spend [several] days in Asia [province]. If possible, he wanted to arrive in Jerusalem by the [time of the] Pentecost festival, [and the time of that festival was near].
Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
17 [When the ship arrived at] Miletus, Paul sent [a messenger] to Ephesus to ask the elders of the congregation to come to talk with him.
Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
18 When the elders arrived, Paul said to them, “You personally know how I [conducted myself among you the entire time] that I was with you, from the first day when I arrived [here] in Asia [province until the day I left].
Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
19 [You know how] I was serving the Lord [Jesus] very humbly and how I sometimes wept [about people. You also know how] I suffered because the Jews [SYN] [who were not believers often] tried [to harm me].
Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
20 You also know that, as I preached [God’s message] to you, I never left out anything that would help you. You know that I taught you [God’s message] when many people were present, and I [also went to your] homes and taught it there.
Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
21 I preached both to Jews and to non-Jews, telling them [all] that they must turn away from their sinful behavior. [I also told them they should] believe in our Lord Jesus.”
Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
22 “And now note this: I am going to Jerusalem, because [God’s] Spirit has clearly shown me that I must go there. I do not know what will happen to me [while I am there].
“Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
23 But I do know that in each city [where I have stopped], the Holy Spirit has (told me/[caused the believers to] tell me) that [in Jerusalem] people will put me in prison [PRS] and will cause me to suffer [PRS].
Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
24 But I do not care even if people kill me, if first I am able to finish the work [MET] that the Lord Jesus has told me [to do. He appointed me] to tell people the good message that God [saves us] by doing for us what we do not deserve.
Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
25 I have preached to you the message about how God desires to rule [people’s lives]. But now I know that today is the last time that you fellow believers will see me [SYN].
“Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
26 So I want you all to understand that if anyone [who has heard me preach] dies [without trusting in Jesus], it is not my fault [MTY],
Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
27 because I told you [LIT] everything [HYP] that God has planned for us [(inc)].
Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
28 [You leaders] must continue to believe and obey [God’s message. You must also help] all the other believers [MET] for whom the Holy Spirit has caused you to be responsible [MTY]. Watch over [MET] yourselves and the other believers [as] a shepherd [watches over his sheep]. God bought them with the blood [that flowed from] his [Son’s body on the cross].
Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
29 I know [very well] that after I leave, [people who teach] [MET] [false doctrines] will come among you and will do great harm to the believers. [They will be like] fierce wolves [that kill sheep].
Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
30 Even in your own group of believers there will be some who will deceive [other] believers by teaching them messages that are false. They will teach those messages so that some people [will believe them and] will become their followers.
Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
31 So watch out [that none of you stops believing the true message about our Lord Jesus]. Remember that day and night for [about] three years I repeatedly taught you that message, and warned you with tears [in my eyes not to believe any other message].”
Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
32 “[Now as I leave you], I ask God to protect you and to keep you believing the message [that he saves us(inc)] by doing for us what we do not deserve. [If you continue believing] the message [that I told you], you will become [spiritually mature], and God will give you the blessings that he has promised to give to all of those who belong to him.
“To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
33 [As for myself], I have not desired anyone’s money [MTY] or [fine] clothing.
Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
34 You yourselves know that I have worked [with my hands] [MTY] to earn the money that my companions and I needed.
Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
35 In everything that I did, I showed you that we [(inc)] should work hard in order [to have enough money] to give some to those who are needy. We [(inc)] should remember that our Lord Jesus himself said, ‘You are happy when people give you what you need, but God will be happy with you when you give other people what they need.’”
Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
36 When Paul had finished speaking, he knelt down with all of the elders and prayed.
Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
37 They all cried a lot, and they hugged Paul and kissed him.
Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
38 They were especially sad because he had said that they would never see him [SYN] again. Then they [all] went with him to the ship.
Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.

< Acts 20 >