< Acts 1 >

1 [Dear] Theophilus, In my first book [that I wrote for you], I wrote about many of the things that Jesus did and taught
Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
2 until the day on which he was taken {[God] took him} up [to heaven]. Before [he went to heaven], saying what the Holy Spirit [told him], he told the apostles whom he had chosen [the things that he wanted them to know].
har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3 After he had suffered [and died on the cross], [he became alive again]. As he appeared to them [often] during [the next] 40 days, the apostles saw him many times. He proved to them in many ways that he was alive again. He talked [with them] about [how] God would rule [MET] [the lives of people who accepted him as their king].
Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4 [One time] while he was with them, he told them, “Do not leave Jerusalem [yet]. Instead, wait [here] until my Father sends [his Spirit] [MTY] [to you], as he promised [to do]. You have heard me speak [to you] about that.
Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
5 John baptized people in water [because they said that they wanted to change their lives], but after a few days [LIT] [God] will put the Holy Spirit within you(pl) [to truly change your lives].”
cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
6 One day when the [apostles] met together [with Jesus], they asked him, “Lord, will you [(sg)] now become the King [MET] over [us] Israelite people [like King David, who ruled long ago]?” (OR, “Lord, will you [(sg)] now [defeat the Romans and] restore the kingdom [to us] Israelite people?”)
Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7 He replied to them, “You do not [need] to know the time [periods] and days [when that will happen]. My Father alone has decided [when he will make me king].
Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8 But [you do need to know that] the Holy Spirit will make you [spiritually] strong when he comes to live in you. Then you will [powerfully] tell people about me in Jerusalem and in all [the other places in] Judea [district], in Samaria [district], and in places far away all over [IDM] the world.”
Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9 After he said that, he was taken {[God] took him} up [to heaven], while they were watching. [He went up into] a cloud [PRS], which prevented them from seeing him [any more].
Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
10 While [the apostles] were [still] staring towards the sky as he was going up, suddenly two men who were wearing white clothes stood beside them. [They were angels].
Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
11 One [of] them said, “You men from Galilee [district], (you do not need to stand [here any longer] looking up at the sky!/why do you still stand [here] looking up at the sky?) [RHQ] [Some day] this same Jesus, whom [God] took from you up to heaven, will come back [to earth]. He will return in the same manner as you [just now] saw him when he went up to heaven, [but he will not return now].”
Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
12 Then [after the two angels left], the apostles returned to Jerusalem from Olive [Tree] Hill, which was about (a half mile/one kilometer) [MTY] from Jerusalem.
Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
13 When they entered [the city], they went upstairs to the room [in the house] where they were staying. [Those who were there included] Peter, John, James, Andrew, Philip, Thomas, Bartholomew, Matthew, [another] James [the son] of Alphaeus, Simon who belonged to the group that wanted to expel the Romans, and Judas [the son] of [another man named] James.
Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
14 All these apostles agreed concerning the things about which they continually were praying [together. Others who prayed with them] included the women [who had accompanied Jesus], Mary who was Jesus’ mother, and his [younger] brothers.
Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15 During those days Peter stood up among his fellow believers. There were [at that place] a group of about 120 of [Jesus’ followers]. Peter said,
A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
16 “My fellow believers, [there are words that King] David wrote [MTY] in the Scriptures long ago that needed to be fulfilled {to happen [as he said they would]}. The Holy Spirit, [who knew that Judas would be the one who would fulfill those words], told David what to write.
'' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17 [Although] Judas had been chosen {[Jesus] had chosen Judas}, along with [the rest of] us [(exc)] to serve [as an apostle], Judas was the person who led to Jesus the people who seized him.”
Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
18 [The Jewish leaders] gave Judas money when he [promised to] treacherously/wickedly [betray Jesus. Later Judas returned that money to them]. When Judas [hanged himself], his body fell down [to the ground]. His abdomen burst open, and all his intestines spilled out. [So] the [Jewish leaders] bought a field [using] that money.
(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
19 All the people who reside in Jerusalem heard [about that], so they called that field in their own [Aramaic] language, Akeldama, which means ‘Field of Blood’, [because it was where someone bled and died].
Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
20 [Peter also said], “[I perceive that what happened to Judas is like what the writer of] Psalms [desired to happen]: ‘May his house become deserted, and may there be no one to live in it.’ (OR, ‘[Judge him, Lord, so that neither he nor] anyone [else] may live in his house!)’ And it seems that [these other words that David wrote also refer to Judas: ] ‘Let someone else take over his work as a leader.’”
“Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21 “So it is necessary [for us apostles] to choose a man [to replace Judas. He must be one who] accompanied [MTY] us all the time when the Lord Jesus was with us.
Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
22 [That would be] from [the time when] John [the Baptizer] baptized [Jesus] until the day when Jesus was taken {when [God] took Jesus} from us up [to heaven]. He must be one who saw Jesus alive again [after he died].”
farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
23 So the [apostles and other believers] suggested [the names of two men who qualified. One man was] Joseph, who was called {whom people called} Barsabbas (OR, Joseph Barsabbas) who [also] had the [Roman] name Justus. The other man was Matthias.
Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24 Then they prayed like this: “Lord [Jesus], Judas stopped being an apostle. [He died and] went to the place where he [deserved to be] [EUP]. [So we(exc) need to choose someone] to replace [Judas in order] that he can serve [you(sg) by becoming] an apostle. You [(sg)] know what everyone is really like. So [please] show us which of these two men you have chosen.”
Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
26 Then they cast lots [to choose between the two of] them, and the lot fell for Matthias. (OR, Then [one of] the [apostles] shook [in a container] small objects/stones [that] they [had marked to determine which man God had chosen]. And the small object/stone [that they had marked] for Matthias fell [out of the container]). So Matthias was considered {they considered Matthias} [to be an apostle] along with the [other] eleven apostles.
suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.

< Acts 1 >