< 2 Chronicles 25 >

1 Amaziah was 25 years old when he became the king [of Judah], and he ruled from Jerusalem for 29 years. His mother was Jehoaddin; she was from Jerusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Amaziah did many things that pleased Yahweh, but he did not do them enthusiastically.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 As soon as he was in complete control of his kingdom, he caused to be executed the officials who had murdered his father.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 But he did not command their sons to be executed; he obeyed what was in the laws that Moses had written. In those laws Yahweh had commanded, “People must not be executed because of [what] their children [have done], and children must not be executed for [what] their parents [have done]. People must be executed only for the sins that they themselves have committed.”
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Amaziah summoned the men of [the tribes of] Judah and Benjamin to come to Jerusalem, and there he put them in groups, each clan in a group by themselves. Then he appointed officers to command each group. Some officers commanded 100 men and some commanded 1,000 men. They counted the men who were at least 20 years old; altogether there were 300,000 men. They were all men who were prepared to be in the army, and able to [fight well, ] using spears and shields.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Amaziah also hired 100,000 capable soldiers from Israel and paid almost four tons of silver for them.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 But a prophet came to him and said, “Your majesty, you must not allow those soldiers from Israel to march with your soldiers, because Yahweh does not help the people of the tribe of Ephraim or from [anywhere else in] Israel.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Even if your soldiers go and fight courageously in battles, God will cause your enemies to defeat you; do not forget that God has the power to help armies or to cause them to be defeated.”
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Amaziah asked that prophet, “If I do that, what about the huge amount of silver that I paid to hire those soldiers from Israel?” The prophet replied, “Yahweh is able to pay you back more money than you paid [to hire those soldiers].”
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 So Amaziah told those soldiers from Israel to return home. They left to go home, but they were very angry with the king of Judah [for not allowing them to stay and fight].
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Then Amaziah became brave, and he led his army to the Salt Valley. There they killed 10,000 men from the Edom people-group.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 The army of Judah also captured 10,000 others, and took them to the top of a cliff and threw them all down over the cliff, with the result that their corpses were all smashed to pieces.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 While that was happening, the soldiers from Israel whom Amaziah had sent home after not allowing them to fight along with his soldiers, raided cities and towns in Judea, from Samaria [city] to Beth-Horon [town]. They killed 3,000 people and took away a great amount of valuable things.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 When Amaziah returned [to Jerusalem] after his army had slaughtered the soldiers from Edom, he brought the idols that were worshiped by the people of Edom. He set them up to be his own gods. Then he bowed down to [worship] them and offered sacrifices to them.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Because of that, Yahweh was very angry with Amaziah. He sent a prophet to him, who said, “Why do you worship these foreign gods that were not even able to save their own people when your army attacked them?”
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 While he was still speaking, the king said to him, “We certainly did not appoint you to be one of my advisors. So stop [talking]! If you say anything more, [I will tell my soldiers to] kill you!” So the prophet said, “I know that God has determined to get rid of you, because you have [begun to] worship idols, and have not heeded my advice.” Then the prophet said nothing more.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Some time later Amaziah, the king of Judah, consulted his advisors. Then he sent a message to Jehoash, the king of Israel. He wrote, “Come here and let’s talk together.”
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 But Jehoash replied to King Amaziah, “One time a thistle growing [in the mountains] in Lebanon sent a message to a cedar tree saying, ‘Let your daughter marry my son.’ But a wild animal in Lebanon came along and trampled the thistle under its feet.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 [The meaning of what I am saying is that] you are saying to yourself that your army has defeated the army of Edom, so you have become very proud. But you should stay at your home. It would not be good for you to cause trouble, which would result in you and your kingdom of Judah being destroyed.”
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 But Amaziah refused to heed Jehoash’s message. That happened because God wanted Jehoash’s army to defeat them, because they were worshiping the gods of Edom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 So Jehoash’s army attacked. Their two armies faced each other at Beth-Shemesh [city] in Judah.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 The army of Judah was badly defeated by the army of Israel, and all the soldiers of Judah fled to their homes.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 King Jehoash’s army also captured King Amaziah there. Then he brought Amaziah to Jerusalem, and his soldiers tore down the wall [that was around the city], from the Ephraim Gate to the Corner Gate. That was a section that was about 600 feet long.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 His soldiers also carried away the gold and silver and other valuable furnishings from the temple which the descendants of Obed-Edom had previously been guarding. They also took away the valuable things in the palace, and they took to Samaria some prisoners whom they had captured.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 King Jehoash of Israel died, and King Amaziah of Judah lived for 15 years after that.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 An account of all the other things that Amaziah did while he was the king [of Judah] is written in the scroll called ‘The History of the Kings of Judah and Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 From the time that Amaziah started to disobey Yahweh, some men in Jerusalem planned to kill him. He was able to escape to Lachish [city], but those who wanted to kill him sent another group of people to Lachish and killed him there.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 They put his corpse on a horse and brought it back to Jerusalem and buried it where his ancestors [had been buried] in the part of Jerusalem called ‘The City of David’.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< 2 Chronicles 25 >