< 2 Chronicles 24 >

1 Joash was seven years old when he became the king [of Judah], and he ruled in Jerusalem for 40 years. His mother’s name was Zibiah; she was from Beersheba [city].
Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
2 Joash did what pleased Yahweh as long as Jehoiada was [the Supreme] Priest.
Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
3 Jehoiada chose two women to be Joash’s wives. And they bore Joash sons and daughters.
Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
4 Some years later, Joash decided that the temple should be repaired.
Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
5 He summoned the priests and other descendants of Levi and said to them, “Go to the towns in Judah and collect from the people the tax money that they are required to pay each year, and use that money to pay for repairing the temple. Do it immediately.” But the descendants of Levi did not do it immediately.
Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
6 So the king summoned Jehoiada and said to him, “Why have you not required the descendants of Levi to bring to Jerusalem from various places in Judah the annual/yearly tax that Moses said that the people of Judah must pay, for taking care of the Sacred Tent?”
Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
7 [The temple needed to be repaired] because the sons of that wicked woman Athaliah had entered into the temple [and had wrecked some of the things], and had also used some of the sacred items that were in it for [the worship of] Baal.
Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
8 So, obeying what the king commanded, the descendants of Levi made a chest and placed it outside the temple, at one of the entrances.
Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
9 Then the king sent letters everywhere in Judah, requesting everyone to bring their tax money to the temple, like Moses had required the Israeli people to do [when they were] in the desert.
Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
10 All the officials and the other people [agreed, and they] brought their contributions gladly. They put the money into the chest until it was full.
Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
11 Whenever the descendants of Levi brought the chest to the king’s officials, and they saw that there was a lot of money in it, the king’s secretary and the assistant to the [Supreme] Priest would take all the money from the chest, and then put the chest back in its place. They did this frequently, and they collected a huge amount of money.
Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
12 The king and Jehoiada gave the money to the men who were supervising the work of repairing the temple. Those men hired stoneworkers and carpenters to repair the temple. They also hired men who worked with iron and bronze to repair things in the temple [that were broken].
Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
13 The men who did the repair work worked hard, and the work of repairing the temple progressed. They rebuilt the temple so that it was like it was originally, and they even made it stronger.
Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
14 When they had finished the repair work, they brought to the king and to Jehoiada the money that they had not used for the repairs. That money was used to make things to use for offering the sacrifices that were completely burned [on the altar], and to make bowls and other gold and silver things for the temple. As long as Joash lived, the people continually brought to the temple sacrifices that were to be completely burned on the altar.
Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
15 Jehoiada lived to become very old. He died when he was 130 years old.
Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
16 He was buried where the kings had been buried, in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’. [He was buried there] because of the good things that he had done in Judah for God and for God’s temple.
Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
17 After Jehoiada died, the leaders of Judah went to Joash, bowed in front of him, and persuaded him to do what they wanted.
Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
18 So they and the other people stopped worshiping at the temple, and they started worshiping the poles dedicated to [the goddess] Asherah and other idols. Because of their doing those sinful things, God was very angry with the people of Jerusalem and [with the people in other places in] Judah.
Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
19 Although Yahweh sent prophets to persuade them to return to him, and although the prophets told them about the evil things that they had done, the people would not pay attention.
Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
20 Then God’s Spirit came upon Zechariah, the son of Jehoiada the [Supreme] Priest. He stood up front of the people and said, “This is what God says: ‘Why are you disobeying what I, Yahweh, have commanded? You have abandoned me, so I will abandon you.’”
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
21 But the people planned to kill Zechariah. And the king joined them in doing it. The people killed Zechariah by throwing stones at him in the temple courtyard.
Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
22 King Joash had forgotten about how Zechariah’s father Jehoiada had been kind to him. That’s why he gave orders for the people to kill Jehoiada’s son Zechariah, who said as he was dying, “I hope that Yahweh will see [what you are doing to me] and punish [you for doing it].”
Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
23 Near the end of that year (OR, early in the following year), the army of Syria marched to attack [the army of] Joash. They invaded Judah and attacked Jerusalem and killed all the leaders of the people. They [seized many valuable things and] sent them to their king in Damascus, [their capital city.]
Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
24 The army of Syria [that came to Judah] was very small, but Yahweh allowed them to defeat the large army of Judah, because he was punishing Joash and the other people of Judah for having abandoned him, the God whom their ancestors worshiped.
Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
25 Before the battle ended, Joash was severely wounded. Then his officials decided to kill him for murdering Zechariah, the son of Jehoiada the [Supreme] Priest. They killed him while he was in his bed. He was buried in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’, but they did not bury him in the place where the other kings had been buried.
Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
26 Those who conspired to kill him were Zabad the son of Shimeath, who was a woman from the Ammon [people-group], and Jehozabad the son of Shimrith, who was a woman from the Moab [people-group].
Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
27 An account of the things that were done by the sons of Joash and the many prophecies about Joash and what he did to repair the temple are written in the scroll called ‘the History of the Kings [of Judah and Israel]’. Then after Joash died, Amaziah his son became the king.
Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chronicles 24 >