< 1 Samuel 9 >

1 There was a rich and influential man whose name was Kish. He belonged to the tribe descended from Benjamin. Kish was the son of Abiel and the grandson of Zeror. He was from the family of Becorath and from the clan of Aphiah.
An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
2 Kish had a son whose name was Saul. He was more handsome than any of the other Israeli men, and he was a head/foot taller than any of the other Israeli men.
Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
3 One day, some of Kish’s female donkeys wandered off. So Kish told Saul, “Take one of my servants with you, and go and search for the donkeys!”
To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
4 So Saul did that. He took a servant, and they walked through the hilly area where the descendants of Ephraim lived, and then they went through the areas named Shalishah and Shaalim, and then they went through all the area where the descendants of Benjamin lived, but they could not find the donkeys.
Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
5 Finally, they came to the area of Zuph. Then Saul said to the servant, “Let’s go back home. If we do not do that, my father will stop worrying about the donkeys and start worrying about us.”
Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
6 But the servant said, “I have another idea [IDM]. There is one of God’s prophets who lives in this town. People respect him very much, because everything he predicts comes true. Let’s go [talk] to him. Perhaps he can tell us where we can go [to find the donkeys].”
Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
7 Saul replied to the servant, “If we go talk with him, [we should give a gift to him, but] what can we give to him? We have no more food in our sacks. Do we have anything else to give to him?”
Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
8 The servant replied, “Look [at this]! I have a small silver coin. I can give this to him, and then he will tell us where to go [to find the donkeys].”
Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
9 Saul said, “Okay, let’s go [talk to him.”] So they went to the town where the prophet lived. As they were going up the hill into the town, they met some young women who were coming out of the town to get some water [from a well]. One of them asked the women, “Is the seer in the town [today]?” [They said that because] previously, if people [in Israel] wanted a message from God, they would say, “Let’s go to the seer,” and people who now are called prophets were at that time called ‘those who see [(visions from God/all that God sees)].’
(A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
12 The women replied, “Yes, he is in the town. In fact, he is [walking on the road] ahead of you. He has just arrived in the town, because the people are going to offer a sacrifice on the altar where the people gather [to worship God].
’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
13 If you go quickly, you will [have time to talk to him] before he goes there. The people who have been invited will not start eating until he arrives there and (blesses/asks God to bless) the sacrifice.”
Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
14 So Saul and the servant entered the town. As they went through the gates, they saw Samuel as he was coming toward them, on the way to where people were going to offer sacrifices.
Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
15 On the previous day, Yahweh had told Samuel,
Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
16 “At this time tomorrow, I will send to you a man from the land where the descendants of Benjamin live. Pour olive oil on his [head] to [indicate that he will] be the leader of my Israeli people. I have seen that my people are suffering [because the Philistine people are oppressing them], and I have heard my people as they have called out to me [for help]. The man on whose [head] you pour olive oil will rescue my people from the [MTY] Philistine people.”
“Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
17 When Samuel saw Saul, Yahweh said to him, “This is the man I told you about yesterday! He is the one who will rule my people!”
Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
18 Saul saw Samuel as he was sitting at the town gateway [but he did not know that it was Samuel]. He went over to him and asked him, “Can you tell me, where is the house of the man who sees [(visions from God/all that God sees)]?”
Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
19 Samuel replied, “I am that man. Go ahead of me with your servant to the place where the people make sacrifices. Both of you will eat with me today. Tomorrow morning I will tell you what you are wanting to know, and then I will send you home.
Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
20 Also, do not worry any more about those donkeys that wandered away three days ago. (Someone has found them/They have been found). But [what you need to know is that] it is you and your family that all the Israeli people are wanting!” [RHQ]
Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
21 Saul replied, “I am from the tribe of Benjamin [RHQ]. That is the smallest tribe in Israel [RHQ]! And my family is the least important family in our tribe! So why are you talking to me like this, [about the Israeli people wanting me and my family]?”
Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
22 Then Samuel brought Saul and the servant into the big dining room, and told them to sit at the head [of the table, indicating that he was] honoring them more than he was honoring the 30 people who had been invited.
Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
23 Then Samuel told the cook, “Bring to me the special piece [of meat] that I told you to set aside.”
Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
24 So the cook brought the leg and the meat that was on it, and set it in front of Saul, [even though those portions were for only the priest to eat]. Samuel said to Saul, “Start eating it. I told the cook to save this for you, so that you could eat it at this time, when all these people whom I invited are here.” So Saul and Samuel ate together.
Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
25 After they finished eating, they returned to the town. Then Samuel took Saul up to the [flat] roof [of his house], and fixed a bed for him.
Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
26 As the sun was rising the next morning, Samuel called up to Saul, “Get up! It is time for me to send you on the road back home.” So Saul got up, and [later] Samuel and Saul left the house together.
Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
27 When they got to the edge of the town, Samuel told Saul to send his servant ahead. After the servant left, Samuel said to Saul, “Stay here for a few minutes, in order that I can give you a message I received from God.”
Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”

< 1 Samuel 9 >